• English
  • Business News
Monday, July 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Na Sa Dokar Ta-ɓaci A Sashen Ilimin Jihar Zamfara – Gwamna Dauda Lawal

by Leadership Hausa
1 year ago
in Ilimi
0
Abin Da Ya Sa Na Sa Dokar Ta-ɓaci A Sashen Ilimin Jihar Zamfara – Gwamna Dauda Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana cewa koma-bayan da aka samu a harkar ilimin jihar a baya ta sa ya ayyana dokar ta-ɓaci a sashen.

Ya kuma nunar da cewa ilimi wani ginshiƙi ne mafi muhimmanci ga ci gaban jihar Zamfara.

A Larabar nan ne ɗaliban makarantar ‘Leadsprings International Schools’ suka karrama Gwamna Lawal a gidan gwamnati da ke Gusau.

Kamar yadda yake ƙunshe a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa waɗannan yara sun kuma miƙa wa Gwamnan wasu buƙatu guda bakwai masu muhimmanci, waɗanda su ke sa ran cimma a nan gaba.

Malam Idirs Bala ya ce, waɗannan tsammani da ake son cimma a aƙibar Zamfara, sun haɗa da babban birnin jihar, Gusau; sashen kiwon lafiya; harkar jiragen sama na Zamfara; fasaha; noma da sashen tattalin arziki, masana’antu da kamfanoni.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

Cikin jawabin da ya yi wa waɗannan yara, Gwamna Dauda ya ƙara jaddada aniyarsa ta yin garambawul a harkar ilimi a jihar.

Gwamnan ya ce, “Ilimi ne abu na ɗaya cikin muhimman abubuwan da gwamnatina ta sanya a gaba, na biyu kuma, shi ne harkar tsaro. Sai dai harkar ilimin mu ba ta tafiya yadda ya kamata a lokutan baya. A kowane lokaci jihar Zamfara tana zamowa ta ƙarshe a harkar ilimi, wannan ne ya sa na sanya dokar ta-ɓaci a harkar ilimin.

zamfara

“Matakan sun haɗa da ɗaukar ƙwararrun Malaman da suka cancanta, samar da gine-gine da isassun kayan aiki, tare kuma da samar da hanyoyin koyarwa irin na zamani.

“Gwamnatina ba za ta gajiya ba, wajen sake fasalin harkar ilimi, ta yadda zai biya buƙatun al’ummarmu.

Daga nan kuma sai Gwamnan ya nuna jin daɗin sa bisa irin misalin ingantaccen ilimin da yaran suka nuna masa sun samu a makaranar tasu. Ya kuma gode wa Hukumar wannan makaranta ta ‘Leadsprings International School’ bisa wannan karramawa da suka yi masa.

zamfara

“Na ji daɗi da ganin irin yanayin karatunku da kuka nuna mana, wannan ya na nuni da cewa ɗaliban makarantar ‘Leadsprings International School’ a shirye suke su goga kafaɗa da kowa a faɗin duniyar nan.

“Ina godiya da wannan karramawa. Gwamnati na za ta ƙarfafa maku a duk inda za ta iya. Ina kira ga sauran makarantu masu zaman kansu su kwaikwayi wannan kyakkyawan aiki na ku.

Cikin nasa jawabin sa, mai makarantar ‘Leadsprings International School, Danjuma Sule ya bayyana cewa makarantarsa a shirye ta ke ta tafi da tsarin ilimin gwamnatin jihar Zamfara.

“Muna jinjina ga gwamnatin ka bisa irin jajircewarta wajen samar da yanayin karatu mai kyau a duk faɗin jihar. Muna kuma godiya da aniyar ka ta ɗaukaka ilimin mata a jihar. Yanzu haka, makarantar ‘Leadsprings International Schools’ muna da ɗalibai mata 386 a ajujuwa daban-daban, kuma muna nan muna nuna masu hanyoyin da za su zama masu amfani ga ci gaban Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Dauda LawalHutun KaratuIlimiMakarantaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Jaddada Bukatar Hadin Gwiwa A Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Na MDD

Next Post

“Tutar Dimokuradiyya” Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace

Related

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 day ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

1 day ago
Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50
Ilimi

Jami’ar Ilorin Ta Karrama Shugabannin JAMB, THISDAY Da Wasu 63 A Bikin Shekara 50

2 days ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano
Ilimi

Ƴansanda Sun Kama Ɗalibai 11 Kan Kisan Wasu Ɗalibai 2 A Kano

3 days ago
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya
Ilimi

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

4 days ago
An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano
Ilimi

An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

4 days ago
Next Post
Amurka

"Tutar Dimokuradiyya" Da Kasar Amurka Ta Rike Ta Lalace

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

Kamfanonin Kera Kayan Likitanci Na Duniya: Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Kasar Sin Babban Ginshiki Ne

July 20, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

‘Ka Da Ki Kuskura Ki Zo Majalisar Tarayya’, Majalisar Dattawa Ta Sake Yi Wa Natasha Gargaɗi

July 20, 2025
An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

An Rufe Bikin Baje Koli Na CISCE Karo Na Uku

July 20, 2025
Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

Cutar Kansa: Uwargidan Gwamnan Zamfara, Ta Zama Sakatariyar Ƙungiyar FLAC

July 20, 2025
Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

Jimillar Sayar Da Kayayyakin Masarufi Ta Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Triliyan 50 A Bana

July 20, 2025
Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

Mataimakin Shugaban Kamfanin Panasonic: Kamfanonin Sin Dake Samar Da Sassan Kayayyaki Ga Kamfaninsa Sun Kai Dubu 6

July 20, 2025
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

July 20, 2025
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

July 20, 2025
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

July 20, 2025
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.