• English
  • Business News
Saturday, August 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

by Abubakar Sulaiman
1 month ago
in Labarai
0
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Ministan Shari’a na Tarayya kuma ɗan jihar Kebbi, Abubakar Malami (SAN), ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC, yana mai cewa matakin ya biyo bayan tattaunawa mai zurfi da kuma nazari na ƙashin kai. A wata sanarwa da ya fitar ranar 2 ga Yuli, 2025, Malami ya bayyana komawarsa jam’iyyar ADC – jam’iyyar da ke jagorantar sabuwar haɗakar jam’iyyun adawa.

Malami ya ce ba fushi ko son mulki ne ya jawo masa wannan mataki ba, illa kawai damuwa da ƙaunar ƙasa da kuma wahalhalun da al’ummar Nijeriya ke ciki. Ya bayyana cewa Nijeriya na cikin mawuyacin hali, inda rashin tsaro ya yi kamari, musamman a Arewacin ƙasa, yayin da gwamnati ke fifita siyasa akan tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a.

  • Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
  • Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

Ya kuma caccaki halin da tattalin arziƙin ƙasa ke ciki, yana mai cewa hauhawar farashin kayan masarufi da rashin aikin yi sun kai matakin da talakawa ba sa iya ciyar da iyalansu. Ya zargi gwamnati da watsi da shugabanci, inda ya ce rabon muƙamai da aiwatar da manufofi yanzu yana bisa biyayya ta siyasa, ba ƙaunar ƙasa ba.

A ƙarshe, Malami ya ce matakin da ya ɗauka na komawa ADC wata hanya ce ta dawo da adalci, da cancanta, da haɗin kai da farfado da ƙasa.

Ya tabbatar wa mutanen jihar Kebbi da cewa zai ci gaba da kasancewa da su, yana kare muradunsu da muradun Nijeriya gaba ɗaya. Ya yi kira ga ’yan Nijeriya su haɗu don ceto ƙasar daga durƙushewa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ADCAPCMalami
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Next Post

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Related

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
Labarai

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

3 hours ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

4 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Labarai

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

5 hours ago
Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar
Labarai

Akwai Bukatar Samar Da Sauyin Zaman Lafiya Mai Dorewa A Duniya — Maryam Bukar

7 hours ago
UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya
Labarai

UBEC Ta Kaddamar Da Makarantun Zamani 21 A Sassan Nijeriya

8 hours ago
Gwamnatin Katsina Za Ta Samu Kudaden Bunkasa Ilimi
Labarai

Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari

9 hours ago
Next Post
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

Wang Yi: Ya Kamata A Mutunta Tarihi Domin Magance Sake Yin Kuskure

August 15, 2025
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

August 15, 2025
Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

Ya Kamata A Yi Wa Japan Jinyar Cutar “Mantuwar Tarihi”

August 15, 2025
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

August 15, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

CMG Ya Kaddamar Da Bikin Mu’amalar Al’adu Da Jama’a A Hedkwatar MDD

August 15, 2025
Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa

August 15, 2025
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

August 15, 2025
Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

Gasar Wasannin Mutum Mutumin Inji Ta Duniya Ta 2025 Na Gabatar Da Sabbin Fasahohin Zamani

August 15, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Babu Dalilin Da Zai Sa ‘Yan Nijeriya Su Yi Talauci – Tinubu

August 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata A Watan Yuli

August 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.