ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Makarantar Katsina-kwalej Zuwa Ta Horon Malamai (1)

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Katsina

Kwalejin horon Malaman makaranta ko Katsina Kwalej ta Katsina ita ce tsohuwar makaranta a Arewacin Nijeriya wadda aka gina ta. a shekarar 1921 dalibai suka fara karatu a cikinta 1922.

An gina tane da tubulin kasa ne wanda aka kona.Halin da ake ciki yanzu ta zama wurin ziyara ind masu yawo shakatawa suke zuwa su kashe kwarkwatar ido duk lokacin da suka zo Katsina.An maida wurin inda ya kasance wurin tarihi ranar 23 ga Afrilu 1959 inda ake kiran wurin da suna Katsina Museum .Alhaji Sir Abubakar Tafawa Balewa Firayim Ministan Nijeriya na farko da kuma Alhaji Sir Ahmadu Bello Sardauna Sakkwato Firimiyan Arewa duk,sun halarci makarantar.

  • Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Gidauniyar Mangal Ta Dauki Nauyin Yi Wa Mutum 12,300 Masu Cutar Kaba Aiki A Katsina

An gina Kwalejin ne a kofar sauri wadda take cikin birnin Katsina,kafin dai bayyanar ilimin zamani wanda ake kira da suna Boko,ilimin addiin musulunci a wancan lokacin shi ne ake amfani da shi ne ake amfani da shi.Wannan dalilin shi yasa Turawan mulkin mallaka a wancan lokacin suka fuskanci matsala gare su da suke niyyar shigo da ilimin zamani a lokacin,don  haka sai suka bi lamarin,a hankali inda daga baya suka kafa makarantar Katsina Kwalej a shekarar 1922.

ADVERTISEMENT

Hada Arewacin da Kudancin Nijeriya da aka yi a shekarar shi yasa bukatar ilimin zamani ta taso, bayan shekara ashirin da kasancewar su, ba lokacin bangaren Arewa musamman ma lardunan da suke karkashin ta basu da ‘yan asalin wurin wadanda suke da ilimin zamani sosai da har, za’a iya basu mukamin Akawu su yi aiki a ofisoshin gwamnati da kuma sassan. Gwamnan Arewa  Sir Hugh Clifford,shi ya sa aka kafa Kwalejin domin horar da ‘yan Arewa wadanda za su yi aiki a makarantun Lardunan.

An taba jin Sir Clifford yana cewa lokacin da yake bude makarantar da aka sa ma suna Katsina Kwalej cewa babban dalilin kafa ita makarantar shi ne a koyawa Malamai wadanda, “su ma  a matsayinsu na Malamai a gaba watarana sune za su iya kasancewa Shugabanni,wadanda ana sa ran halayensu na iya gyaruwa domin a daidaita al’umma.”Kwalejin Katsina ta fara ne da daukar dalibai 50  wadanda  suke daga Lardunan Arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

A wancan lokacin,Mrs. Bintu M.Sadik, cewa tayi  Sir S.M. Banaman shi ne Shugaban Kwalejin na farko duk kuma Malaman Turawa, daga baya ne aka dauke Hausawa ‘yan asalin wurin saboda su koyar da Hausa da kuma al’amarin daya shafi addinin musulunci.Ta ce mshahuran ‘yan Arewa sun halarci Kwalejin daga cikinsu akwai Firayim Minista na farko Abubakar Tafawa Balewa,Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan  Arewa, da kuma Sir Kashim Ibrahim,  da dai sauran wasu duk sun halarci Kwalejin ta Katsina

An samu labarin kasar Katsina ta taba kasancewa wata babbar cibiyar Kasuwanci ta Sahara. Wannan  shi tun  lokacin da aka hade Arewa da Kudancin Nijeriya Katsina tana daya daga cikin wuraren da  hanyar jirgin kasa ta bi ko kuma Layin Dogo  a lokacin.Sarkin Katsina Muhammadu Dikko shi ya bada wurin da aka gina Katsina Kwalejin ne a cikin gonarsa da ke Rafukka a lokacin.

Katsina
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
Ilimi

Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai

May 31, 2026
Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
Ilimi

Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu

May 30, 2026
Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.