• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa 61 Da Suke Kawo Mutuwar Aure!

byBilkisu Tijjani
2 years ago
Aure

Rayuwar aure an gina ta ne kan nutsuwa da soyayya da tausayi, tsakanin miji da matarsa, tare da fahimtar juna da girmama juna ko mutuntawa da kyakkyawan zama a tsakanin miji da mata ta yadda za su yi rayuwa mai tsawo, ba tare da wani ya shiga hakkin wani ba.

Wannan ya sa shaidan yake kai kawo da zirga zirga da kulle-kulle da kutunguila wajen lalata harkar aure, saboda ya san in aure ya lalace komai zai iya lalacewa sakamakon lalacewar sa. Wannan ya sa Malamai da masu ba da tarbiyya da kuma masu lura da al’amuran al-umma suke kara wayar wa da alumma kai, akan sake-saken sure da kuma hadarinsa wanda sakamakon ya kan haifar da rugujewar gida, tabarbarewar tarbiyya da lalacewar tsaro da rashin zaman lafiyar al-umma. Don haka muka yi nazari bayan bincike da tattaunawa, da wadanda suka shiga irin wadannan matsaloli.

  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Gana Da Tawagar Amurka Ta Rukunin Ayyukan Hada-hadar Kudi Na Sin Da Amurka 
  • Gobara Ta Kone Shagunan Hatsi 19 A Adamawa

Don haka muka fitar da dalilai guda sittin 61 wadanda muke ganin su ne Ummul Haba’ isin wadannan matsaloli wadanda idan ba a kula da suba za a samu mutuwar aure.

Mun kasa wadannan matsaloli zuwa kashi uku 3 : Na daya. Matsalolin da suke faruwa kafin aure. Na biyu, matsalolin da suke faruwa lokacin aure. 3. Matsalolin da ke faruwa bayan aure.

Wadannan matsaloli guda uku a kwai masu zuwa daga bangaren mata, akwai masu zuwa daga bangaren maza, akwai masu zuwa daga duka bangarorin guda biyu.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Don haka cibiya mai Suna “Lobe And Mercy School For Marriage Counseling”

ta dauki wadannan abubuwa daya bayan daya take shirya bitoci a kai.

Al-adu, Rashin Ilimin zamantakewar aure, rashin zabo matar kirki tagari, Auren da babu soyayya daga miji ko mata. Gaggawar yin aure ba tare da mutum ya shirya ba.

Banbancin Ilimi, Rashin binciken halin miji kafin aure. Rashin binciken halin mata kafin aure, Matsalar iyayen miji, Matsalar iyayen mata, Matsalar dangin miji, Matsalar dangin matar. Rashin tsafta. Rashin iya kwalliya, Rashin iya magana, Rashin ciyarwa, Rashin iya kwanciyar aure, Rashin adalci, Goyon kaka (Yar Shagwaba), Auren kisan wuta, Zaman gidan haya, Ruwan ido wajen neman aure, Auren bariki, Auren mace don kudinta ko danginta, Auren dole, Matsalar talauci.

Matsalar kawaye, Zafin kishi, Rashin haihuwa, Rashin ladabi, Rashin kunya, Shaye-shayen kayan maye, Kannen miji, Kannen amarya, Abokan miji, Sata, Gulma, tsananin damuwa, Rashi lafiyar mace wajen gamsar da miji, Rashin lafiyar miji wajen gamsar da matarshi, Sharrin bokaye. Rashin shawara tsakanin miji da mata, Aikin mace (Ta zama yar kasuwa ko ma’aikaciya, Rashin Ilimi da Samun wayewa akan aure, Rashin daukar nauyin iyali wajen basu hakki.

Cin bashi a yi aure, Yawan tafiye-tafiye (Bala Guro), Yawan zuwa unguwa, Cin amanar aure daga miji ko mata, Shigar da kawaye ko abokai cikin harkar iyali, Rashin kula da addini. Girman kan daya daga cikin ma’aurata.

Rashin daukar aure a matsayin Ibada, Butulci da manta alheri, Samun larura ko wani ciwo mai tsanani, Yawan shigar iyaye cikin harkar aure, Al’mubazzaranci, Rashin godiya, Mummunan zato, da kuma Rashin nuna tausayi da damuwa da juna.

Allah ya daidaita tsakanin ma’aurata ya ba da zaman lafiyar aure, Amin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version