• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

by Abubakar Abba and Sulaiman
4 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Aikin Gona
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fannin aikin noma na bayar da gagarumar gudunmawa a Nijeriya, duba da cewa; akasarin ‘yan kasar, sun dogara ne a kan sana’ar ta noma.

Kazalika, fannin na taimakawa wajen samar da kimanin kashi 23 ga tattalin arzikin kasar.

  • Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina
  • Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu

Sai dai, abin takaici, har yanzu kasar ta dogara ne wajen shigo da kayan abinci cikin kasar, sannan kuma talakawanta da dama na kwana da yunwa sakamakon karancin abinci.

An karawa fannin kashi 127 a cikin kasafin kudi na bana zuwa Naira biliyan 826.5, sabanin yadda ake ware wa fannin Naira biliyan 362.9 a kasafin kudi na 2024, wanda wannan mataki na nuna cewa, gwamnatin tarayya a shirye take, don bunkasa fannin.

Sai dai wasu kwararru a fannin, sun bayyana manyan kalubalen rashin tsaro, sauyin yanayi, tsadar kayan aikin noma da tsadar gudanar da aiki, barkewar cututtukan da kwarin da ke lalata amfanin da aka shuka a matsayin manyan kalubale biyar da suka wajaba a magance su a wannan shekara, domin habaka noma.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Har ila yau, sun bayar da wannan shawara ce, duba da irin rawar da wadannan kalubale biyar ke takawa a lokacin kakar noma ta 2023 da kuma ta 2024.

1- Kalubalen Rashin Tsaro: Wannan matsalar na jawo wa manoma da sauran masu son zuba hannun jari a fannin koma baya, musamman duba da yadda ‘yan bindigar daji ke halaka manoma da kuma yin garkuwa da su da dama a 2024.

Hakan ya haifar da hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kimanin kashi 39.84, musamman a watan Disambar 2024.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, idan har ana bukatar samar da wadataccen abinci a 2025, ya zama wajbi a dauki matakan da suka dace, don kare rayukan manoma da kuma magance yunwa.

Sai dai wasu manoman sun ce, rashin tsaron ya ragu a wasu Jihohin Arewacin Kasar da lamarin ya fi yin kamari.

2. Sauyin Yanayi: Wannan lamari ya zama tamkar ruwan dare a fadin duniya, wanda kuma yake jawo sauya tsarin noma, misali a 2024, wasu manoma a sassan Arewacin Nijeriya, sun koka kan rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci, wanda hakan ya jawo ba su samu wani yin girbi mai kyau ba.

Masana sun yi hasashen cewa, matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, sauyin yanayi zai zama babbar barazana a kakar noma ta 2025, wanda kuma rashin daukar matakan kan iya haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

A cewar wani rahoto na Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FAO), ruwan sama kamar da bakin kwarya da kuma afkuwar annobar ambaliyar ruwan sama a 2024, ya lalata sama da tan miliyan daya na amfanin gona, wanda wannan adadi zai iya ciyar da mutane miliyan 13.

Kazalika, a watan Satumbar 2024, Dam din Alau Dam ya jawo mummunar ambaliyar ruwa, inda ya lalata hakta kimanin 700,000 a cikin kimanin gonaki 200.

Har ila yau, a 2024; sauyin yanayi ya haifar da ambaliyar ruwan sama a Jihohin Borno, Bauchi, Sakkwato da kuma Jigawa.

3- Barkewar Cututtuka A Gonakin Da Kwari Suka Lalata Amfanin Gona: Misali cutar da lalata Citta da cutar murar tsintsaye da kuma cutar da ke lalata tumatir a 2024, sun yi matukar barna.

Akwai cutar da ta lalata wasu gonaki na Citta, wanda adadin kudin suka kai kimanin Naira biliyan 12 a 2023.

Manoma sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a dauki matakan gaggawa tare da samar da dauki, domin dakile wadannan cututtuka a 2025.

4- Tsadar Farashin Kayan Gudanar Da Aikin Noma: Manoma sun fuskanci hauhawar farashin kayan da ake gudanar da aikin noma.

Wata kididdiga ta nuna cewa, farashin Man Fetur na haifar da hauhawar farashin kayan abinci, sannan kuma manoma da ‘yan kasuwa sun koka kan haramtaccen harajin na ‘yan na kama ke kakaba musu, bayan sun yo jigilar amfanin gona.

5- Hauhawar Farashin Kayan Noma: Tsadar farashin takin zamani, injinan ban ruwa, tsadar Irin noma, sun kasance manyan kalubale ga manoma, wanda hakan kuma ke shafar girbin amfanin gona.

Saboda tsadar ingantaccen Irin noma, hakan ya tilasta wa manoma sayen Iri, wanda ba shi da wani inganci.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a 2025, a kawo karshen wannna matsalar, domin samar da wadataccen abinci a kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina

Next Post

An Kama Miyagun Kwayoyi Kan Hanyar Zuwa Birtaniya A Filin Jiragen Saman Legas

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

3 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

3 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

3 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

1 week ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

1 week ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

An Kama Miyagun Kwayoyi Kan Hanyar Zuwa Birtaniya A Filin Jiragen Saman Legas

LABARAI MASU NASABA

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.