ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Nijeriya

Rahotanni sun bayyana cewa, annobar cutar murar tsintsaye (Bird flu), ta bazu a Jihohin Filato da Katsina.

A makwanni biyu da suka gabata ne, Gwamnatin Tarayya ta ankarar da masu kiwo, musamman na tsintsaye da ofis-ofis na rassan likitocin dabbobi na kasar nan kan barkewar wannan cuta a Jihar Kano.

  • Badakala: Bankin Duniya Ya Kakaba Wa Kamfanoni 2 A Nijeriya Takunkumi
  • NPA Da Kamfanin NLNG Za Su Kulla Hadakar Fitar Da Iskar Gas Ketare

A ranar 23 ga watan Janairun 2025 ne, aka samu rahoton bullar cutar a yankin Farin Gada da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa.

ADVERTISEMENT

Daraktan duba lafiyar dabbobi na Jihar Filato, Dakta Shase’et Sipak Dawat, a cikin sanarwar da ya fitar a jihar ya bayyana cewa, an samu barkewar annobar murar ce ga kajin gidan gona a wani wajen kiwata su, inda cutar ta harbi tsintsaye sama da 3,000.

Dakta Dawat, ya nuna damuwarsa kan yadda mai kiwon tsintsayen da cutar ta shafa ya sayar da su kafin likitocin dabbobi daga Ma’aikatar Aikin Noma da Raya Karkara su ziyarci wajen kiwon nasa, domin daukar matakan da suka dace.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

“Wannan dalili ne yasa, ake shawartar masu kiwon kajin gidan gonar da su kasance masu sanya idanu tare da tabbatar da tsaftace guraren da suke yin kiwon nasu, domin bai wa tsintsayen da suke kiwatawa kariyar da ta kamata”, in ji Dawat.

Bugu da kari, a Jihar Katsina kuwa, wani jami’in kula da lafiyar dabbobi a shiyyar Karamar Hukumar Malumfashi, Dakta Yau Ishaku; a wani sako da ya isar ga masu kiwon tsintsaye a jihar, ya bayyana bullar annonar a jihar, wanda ya sanar da cewa, ta bulla ne a cikin kwana biyu da suka wuce, kafin samun bullar ta a Jihar Filato.

“Cutar ta bulla ne a Jihar Katsina, a ranar 21 ga watan Janairun 2025, sannan kuma yana da muhimmanci ga daukacin masu kiwon tsitsayen a Kananan Hukumomin Malumfashi, Kafur da Kankara da ke karkashin ofishin shiyya a Karamar Hukumar Malumfashi, da su tabbatar da sun kiyaye wajen daukar matakai, domin kare guraren da suke aiwatar da kiwonsu daga kutsawar wannan annona.”

Ya kara da cewa, ya zama wajibi ga masu kiwon da su rika hana barin mutane suna shiga guraren da suka killace, domin kiwon nasu.

Dakta Yau, ya kuma shawarci masu kiwon da su tabbatar da suna tsaftace kayan da suke amfani da su wajen ciyar da tsitsayen da suke kiwatawa, domin kare su daga kamuwa da cututtuka.

Tsuntsaye
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Tsuntsaye
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Aikin Gona

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.