ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Aikin Gona

Fannin aikin noma na bayar da gagarumar gudunmawa a Nijeriya, duba da cewa; akasarin ‘yan kasar, sun dogara ne a kan sana’ar ta noma.

Kazalika, fannin na taimakawa wajen samar da kimanin kashi 23 ga tattalin arzikin kasar.

  • Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina
  • Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu

Sai dai, abin takaici, har yanzu kasar ta dogara ne wajen shigo da kayan abinci cikin kasar, sannan kuma talakawanta da dama na kwana da yunwa sakamakon karancin abinci.

ADVERTISEMENT

An karawa fannin kashi 127 a cikin kasafin kudi na bana zuwa Naira biliyan 826.5, sabanin yadda ake ware wa fannin Naira biliyan 362.9 a kasafin kudi na 2024, wanda wannan mataki na nuna cewa, gwamnatin tarayya a shirye take, don bunkasa fannin.

Sai dai wasu kwararru a fannin, sun bayyana manyan kalubalen rashin tsaro, sauyin yanayi, tsadar kayan aikin noma da tsadar gudanar da aiki, barkewar cututtukan da kwarin da ke lalata amfanin da aka shuka a matsayin manyan kalubale biyar da suka wajaba a magance su a wannan shekara, domin habaka noma.

LABARAI MASU NASABA

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

Har ila yau, sun bayar da wannan shawara ce, duba da irin rawar da wadannan kalubale biyar ke takawa a lokacin kakar noma ta 2023 da kuma ta 2024.

1- Kalubalen Rashin Tsaro: Wannan matsalar na jawo wa manoma da sauran masu son zuba hannun jari a fannin koma baya, musamman duba da yadda ‘yan bindigar daji ke halaka manoma da kuma yin garkuwa da su da dama a 2024.

Hakan ya haifar da hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kimanin kashi 39.84, musamman a watan Disambar 2024.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, idan har ana bukatar samar da wadataccen abinci a 2025, ya zama wajbi a dauki matakan da suka dace, don kare rayukan manoma da kuma magance yunwa.

Sai dai wasu manoman sun ce, rashin tsaron ya ragu a wasu Jihohin Arewacin Kasar da lamarin ya fi yin kamari.

2. Sauyin Yanayi: Wannan lamari ya zama tamkar ruwan dare a fadin duniya, wanda kuma yake jawo sauya tsarin noma, misali a 2024, wasu manoma a sassan Arewacin Nijeriya, sun koka kan rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci, wanda hakan ya jawo ba su samu wani yin girbi mai kyau ba.

Masana sun yi hasashen cewa, matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, sauyin yanayi zai zama babbar barazana a kakar noma ta 2025, wanda kuma rashin daukar matakan kan iya haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

A cewar wani rahoto na Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FAO), ruwan sama kamar da bakin kwarya da kuma afkuwar annobar ambaliyar ruwan sama a 2024, ya lalata sama da tan miliyan daya na amfanin gona, wanda wannan adadi zai iya ciyar da mutane miliyan 13.

Kazalika, a watan Satumbar 2024, Dam din Alau Dam ya jawo mummunar ambaliyar ruwa, inda ya lalata hakta kimanin 700,000 a cikin kimanin gonaki 200.

Har ila yau, a 2024; sauyin yanayi ya haifar da ambaliyar ruwan sama a Jihohin Borno, Bauchi, Sakkwato da kuma Jigawa.

3- Barkewar Cututtuka A Gonakin Da Kwari Suka Lalata Amfanin Gona: Misali cutar da lalata Citta da cutar murar tsintsaye da kuma cutar da ke lalata tumatir a 2024, sun yi matukar barna.

Akwai cutar da ta lalata wasu gonaki na Citta, wanda adadin kudin suka kai kimanin Naira biliyan 12 a 2023.

Manoma sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a dauki matakan gaggawa tare da samar da dauki, domin dakile wadannan cututtuka a 2025.

4- Tsadar Farashin Kayan Gudanar Da Aikin Noma: Manoma sun fuskanci hauhawar farashin kayan da ake gudanar da aikin noma.

Wata kididdiga ta nuna cewa, farashin Man Fetur na haifar da hauhawar farashin kayan abinci, sannan kuma manoma da ‘yan kasuwa sun koka kan haramtaccen harajin na ‘yan na kama ke kakaba musu, bayan sun yo jigilar amfanin gona.

5- Hauhawar Farashin Kayan Noma: Tsadar farashin takin zamani, injinan ban ruwa, tsadar Irin noma, sun kasance manyan kalubale ga manoma, wanda hakan kuma ke shafar girbin amfanin gona.

Saboda tsadar ingantaccen Irin noma, hakan ya tilasta wa manoma sayen Iri, wanda ba shi da wani inganci.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a 2025, a kawo karshen wannna matsalar, domin samar da wadataccen abinci a kasar.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar NEPZA Ta Tabbatar Wa Da Masu Zuba Jari Goyon Bayanta
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
  • Sulaiman
    Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma
  • Sulaiman
    Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin
  • Sulaiman
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

MASU ALAKA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci
Noma Da Kiwo

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
Noma Da Kiwo

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

An Kama Miyagun Kwayoyi Kan Hanyar Zuwa Birtaniya A Filin Jiragen Saman Legas

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.