ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyar Da Ya Kyautu A Mayar Da Hankali A Kansu A Kakar Noman 2025

by Abubakar Abba and Sulaiman
1 year ago
Aikin Gona

Fannin aikin noma na bayar da gagarumar gudunmawa a Nijeriya, duba da cewa; akasarin ‘yan kasar, sun dogara ne a kan sana’ar ta noma.

Kazalika, fannin na taimakawa wajen samar da kimanin kashi 23 ga tattalin arzikin kasar.

  • Annobar Cutar Murar Tsuntsaye Ta Yadu A Jihohin Filato Da Katsina
  • Kashi 85 Na Inibin Da Ake Nomawa Nijeriya, Daga Jihar Kaduna Ne – Dalhatu

Sai dai, abin takaici, har yanzu kasar ta dogara ne wajen shigo da kayan abinci cikin kasar, sannan kuma talakawanta da dama na kwana da yunwa sakamakon karancin abinci.

ADVERTISEMENT

An karawa fannin kashi 127 a cikin kasafin kudi na bana zuwa Naira biliyan 826.5, sabanin yadda ake ware wa fannin Naira biliyan 362.9 a kasafin kudi na 2024, wanda wannan mataki na nuna cewa, gwamnatin tarayya a shirye take, don bunkasa fannin.

Sai dai wasu kwararru a fannin, sun bayyana manyan kalubalen rashin tsaro, sauyin yanayi, tsadar kayan aikin noma da tsadar gudanar da aiki, barkewar cututtukan da kwarin da ke lalata amfanin da aka shuka a matsayin manyan kalubale biyar da suka wajaba a magance su a wannan shekara, domin habaka noma.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

Har ila yau, sun bayar da wannan shawara ce, duba da irin rawar da wadannan kalubale biyar ke takawa a lokacin kakar noma ta 2023 da kuma ta 2024.

1- Kalubalen Rashin Tsaro: Wannan matsalar na jawo wa manoma da sauran masu son zuba hannun jari a fannin koma baya, musamman duba da yadda ‘yan bindigar daji ke halaka manoma da kuma yin garkuwa da su da dama a 2024.

Hakan ya haifar da hauhawar farashin kayan abinci da ya kai kimanin kashi 39.84, musamman a watan Disambar 2024.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, idan har ana bukatar samar da wadataccen abinci a 2025, ya zama wajbi a dauki matakan da suka dace, don kare rayukan manoma da kuma magance yunwa.

Sai dai wasu manoman sun ce, rashin tsaron ya ragu a wasu Jihohin Arewacin Kasar da lamarin ya fi yin kamari.

2. Sauyin Yanayi: Wannan lamari ya zama tamkar ruwan dare a fadin duniya, wanda kuma yake jawo sauya tsarin noma, misali a 2024, wasu manoma a sassan Arewacin Nijeriya, sun koka kan rashin samun saukar ruwan sama a kan lokaci, wanda hakan ya jawo ba su samu wani yin girbi mai kyau ba.

Masana sun yi hasashen cewa, matukar ba a dauki matakan da suka kamata ba, sauyin yanayi zai zama babbar barazana a kakar noma ta 2025, wanda kuma rashin daukar matakan kan iya haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

A cewar wani rahoto na Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Duniya (FAO), ruwan sama kamar da bakin kwarya da kuma afkuwar annobar ambaliyar ruwan sama a 2024, ya lalata sama da tan miliyan daya na amfanin gona, wanda wannan adadi zai iya ciyar da mutane miliyan 13.

Kazalika, a watan Satumbar 2024, Dam din Alau Dam ya jawo mummunar ambaliyar ruwa, inda ya lalata hakta kimanin 700,000 a cikin kimanin gonaki 200.

Har ila yau, a 2024; sauyin yanayi ya haifar da ambaliyar ruwan sama a Jihohin Borno, Bauchi, Sakkwato da kuma Jigawa.

3- Barkewar Cututtuka A Gonakin Da Kwari Suka Lalata Amfanin Gona: Misali cutar da lalata Citta da cutar murar tsintsaye da kuma cutar da ke lalata tumatir a 2024, sun yi matukar barna.

Akwai cutar da ta lalata wasu gonaki na Citta, wanda adadin kudin suka kai kimanin Naira biliyan 12 a 2023.

Manoma sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a dauki matakan gaggawa tare da samar da dauki, domin dakile wadannan cututtuka a 2025.

4- Tsadar Farashin Kayan Gudanar Da Aikin Noma: Manoma sun fuskanci hauhawar farashin kayan da ake gudanar da aikin noma.

Wata kididdiga ta nuna cewa, farashin Man Fetur na haifar da hauhawar farashin kayan abinci, sannan kuma manoma da ‘yan kasuwa sun koka kan haramtaccen harajin na ‘yan na kama ke kakaba musu, bayan sun yo jigilar amfanin gona.

5- Hauhawar Farashin Kayan Noma: Tsadar farashin takin zamani, injinan ban ruwa, tsadar Irin noma, sun kasance manyan kalubale ga manoma, wanda hakan kuma ke shafar girbin amfanin gona.

Saboda tsadar ingantaccen Irin noma, hakan ya tilasta wa manoma sayen Iri, wanda ba shi da wani inganci.

Kwararrun sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi a 2025, a kawo karshen wannna matsalar, domin samar da wadataccen abinci a kasar.

Noma
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B
  • Sulaiman
    CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare
  • Sulaiman
    Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

MASU ALAKA

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

An Kama Miyagun Kwayoyi Kan Hanyar Zuwa Birtaniya A Filin Jiragen Saman Legas

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.