ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

by Bello Hamza
1 year ago
Hajjin Bana

A duk shekara, hukumomin kasar Saudiya na bullo da sabbin tsare-tsare don inganta jin dadin Alhazai da kuma yadda ake gudanar da aikin hajjin.

A shekarun baya an fuskanci rushe -rushe domin fadada wurare ibada masu tsarki inda Alhazai musamman ke yin cincirindo domin gudanar da ayyukan ibada.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC

Rashin issashen wuri ya haifar da mastaloli da dama a shekarun baya inda har aka kai ga rasa rayukan mutane da dama.

ADVERTISEMENT

A wannan shekarar Hukumar Saudi ta bullo da katin tantance mai cikakken izinin kasancewa a wurare masu tsari da ake gudanar da aikin hajji. Katin da aka lakaba wa suna NUSUK ya zama wa wasu mahajjata alakakai, musamman ganin an samu jinkiri daga hukumar Alhazai na ba wasu Alhazai wannan katin, musamman lokacin da aka shigo garin Makkah.

Jami’an tsaron Saudiya sun yi ta kama wadanda ke zirga-zirga ba tare da makale da katin NUSUK a wuyarsu ba. Shiga masallacin harami ya gagari Alhazan da basu da katin NUSUK.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Wannan ya sa hukumar Alhazai ta NAHCON ta kara kaimi wajen ganin ta ba kowa katinsa na NUSUK a kan lokaci.

A bayaninsa na cikakken dalilin bullo da katin NUSUK, wani jami’n tsaro na kasar Saudiya wanda ya nemi mu sakaya sunansa saboda bashi da ikon yin magana da ‘yan jarida, ya ce, a shekarun baya bata gari na shigowa cikin tawagar Alhazai inda suke sace-sace musamman a yayin zaman Muna, Arafat da Muzdalifah, sannan kuma hakan zai taimaka wajen takaita hankoron wadanda basu da izinin gudanar da aikin Hajji shiga wurare masu tsarki inda haka yakan haifar da cunkoso, ga duk wanda ya samu gudanar da aikin hajjin bana zai bayyana maka yadda katin NUSUK ta nastar da shi.

Wannan tsari na NUSUK ya taimaka wajen samun cikakken adadin wadanda suka shigo Saudiya domin aikin hajji da kuma kididdigar daga inda suka shigo. Ma’aikatar aikin Hajji da Umara ta ce, alhazai 1,833,164 suka gudanar da aikin hajjin bana daga sassan duniya sun kuma shigo ne ta hanyoyi daban daban.

Wani abu kuma da ya dauki hankalin duniya gaba daya game da aikin hajjin bana, shi ne irin tsananin zafin ranar da aka yi a ranakun jifar jamra, wanda sai ta kai da hukumar kasar Saudiya, a ta bakin Ministan Umara Hajji Abdulfattah bin Suka bayar da umarnin a dakatar da tafiya jamrat na tsawon awa 5, aka kuma umarci Alhazai su lizimci sha ruwa a kai-kai su kuma guji gararamba a cikin ranar ba tare da wani dalili ba.

Hukumomi su da tabbatar da mutuwar mutum 20 yawancin su daga kasashe yankin nahiyar Asiya.

Duk an kammala aikin Hajjn 2024 hasashe ya nuna cewa, za a ci gaba da fuskantar karin zafin rana inda ake ganin zai iya kaiwa 50 zuwa 60 a ma’aunin zafi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
Labarai

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
'yansanda
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Next Post
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.