• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Biyu Da Suka Fi Daukar Hankali A Hajjin Bana

by Bello Hamza
1 year ago
in Labarai
0
Me Ya Sa Ba A Fara Shekarar Hijirah Da Ranar Badar Ko Ranar Cikar Wahayi Ba? (II)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A duk shekara, hukumomin kasar Saudiya na bullo da sabbin tsare-tsare don inganta jin dadin Alhazai da kuma yadda ake gudanar da aikin hajjin.

A shekarun baya an fuskanci rushe -rushe domin fadada wurare ibada masu tsarki inda Alhazai musamman ke yin cincirindo domin gudanar da ayyukan ibada.

  • Kasar Philippines Na Kara Hauka Kan Batun Tekun Kudancin Kasar Sin
  • A Guji Ajiye Abinci A Firji Fiye Da Kwana 3 – NAFDAC

Rashin issashen wuri ya haifar da mastaloli da dama a shekarun baya inda har aka kai ga rasa rayukan mutane da dama.

A wannan shekarar Hukumar Saudi ta bullo da katin tantance mai cikakken izinin kasancewa a wurare masu tsari da ake gudanar da aikin hajji. Katin da aka lakaba wa suna NUSUK ya zama wa wasu mahajjata alakakai, musamman ganin an samu jinkiri daga hukumar Alhazai na ba wasu Alhazai wannan katin, musamman lokacin da aka shigo garin Makkah.

Jami’an tsaron Saudiya sun yi ta kama wadanda ke zirga-zirga ba tare da makale da katin NUSUK a wuyarsu ba. Shiga masallacin harami ya gagari Alhazan da basu da katin NUSUK.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

Wannan ya sa hukumar Alhazai ta NAHCON ta kara kaimi wajen ganin ta ba kowa katinsa na NUSUK a kan lokaci.

A bayaninsa na cikakken dalilin bullo da katin NUSUK, wani jami’n tsaro na kasar Saudiya wanda ya nemi mu sakaya sunansa saboda bashi da ikon yin magana da ‘yan jarida, ya ce, a shekarun baya bata gari na shigowa cikin tawagar Alhazai inda suke sace-sace musamman a yayin zaman Muna, Arafat da Muzdalifah, sannan kuma hakan zai taimaka wajen takaita hankoron wadanda basu da izinin gudanar da aikin Hajji shiga wurare masu tsarki inda haka yakan haifar da cunkoso, ga duk wanda ya samu gudanar da aikin hajjin bana zai bayyana maka yadda katin NUSUK ta nastar da shi.

Wannan tsari na NUSUK ya taimaka wajen samun cikakken adadin wadanda suka shigo Saudiya domin aikin hajji da kuma kididdigar daga inda suka shigo. Ma’aikatar aikin Hajji da Umara ta ce, alhazai 1,833,164 suka gudanar da aikin hajjin bana daga sassan duniya sun kuma shigo ne ta hanyoyi daban daban.

Wani abu kuma da ya dauki hankalin duniya gaba daya game da aikin hajjin bana, shi ne irin tsananin zafin ranar da aka yi a ranakun jifar jamra, wanda sai ta kai da hukumar kasar Saudiya, a ta bakin Ministan Umara Hajji Abdulfattah bin Suka bayar da umarnin a dakatar da tafiya jamrat na tsawon awa 5, aka kuma umarci Alhazai su lizimci sha ruwa a kai-kai su kuma guji gararamba a cikin ranar ba tare da wani dalili ba.

Hukumomi su da tabbatar da mutuwar mutum 20 yawancin su daga kasashe yankin nahiyar Asiya.

Duk an kammala aikin Hajjn 2024 hasashe ya nuna cewa, za a ci gaba da fuskantar karin zafin rana inda ake ganin zai iya kaiwa 50 zuwa 60 a ma’aunin zafi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbubuwaAlhazaiHajjin Bana
ShareTweetSendShare
Previous Post

NAHCON Ta Gargadi Alhazai Su Guji Tsarabar Ruwan Zamzam 

Next Post

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

6 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

7 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

9 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

11 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

11 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

14 hours ago
Next Post
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Rikicin Sarautar Kano: Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnatin Tarayya, APC Ta Mayar Da Martani

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.