• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Takwas Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bai Wa Fifiko

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana abubuwa guda takwas da gwamnatinsa za ta fi bai wa fifiko wajen bunkasa tattalin arziki da zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ministan Kudi kuma ministan da ke kula da harkokin tattalin arziki, Wale Edun, ya gabatar da tsarin taswirar tattalin arziki, wanda aka yi la’akari da shi a farkon babban taron majalisar zartarwa ta tarayya da ya gudana a wannan mako.

  • Ranar Litinin Za A Kaddamar Da Jirgin Kasan Legas Da Zai Rika Jigilar Fasinja 175,000
  • Sin Na Shirin Sabunta Dabarun Kare Mabambantan Halittu Na Kasa Da Tsare-tsare

Edun wanda ya bayyana wa manema labarai na gidan gwamnati ajandar da suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, damar samun babban jari, inganta tsaro, inganta filin wasan da mutane da kamfanoni za su yi aiki, inganta tsarin dokokin kasa, da yaki da cin hanci da rashawa.

Ya ce majalisar zartarwa ta yi nazari a kan abubuwa takwas da suka fi ba da fifiko tare da gano abubuwan da za a cimma a cikin shekaru uku masu zuwa.

Edun ya ce shugaban kasa ya bai wa ministoci umurnin kan su fitar da manufofi da shirye-shirye a cikin makonni don inganta tattalin arzikin kasa tare da kyautata al’amura ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Edun ya ce majalisar ta amince da cewa tattalin arzikin bai kai inda ya kamata ba.

Game da batun alkiblar majalisar zantarwar ta dosa kuwa, ministan ya ce, “Tun da farko Shugaba Tinubu ya taya kowa murna tare da jaddada babban abin da ‘yan Nijeriya suke bukata, sannan ya karfafa muna gwiwa wajen jajircewa da kuma gudanar da yin aiki cikin gaggawa wajen samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Tun da farko, mun gudanar da wani atisaye na duba inda al’amura suka tsaya dangane da tattalin arziki, hauhawar farashin kayayyaki, hauhawar farashin kudadin waje, rashin aikin yi da sauransu.

“Babban abin da ya dace shi ne, ba inda ya kamata mu kasance ba, mun kuma yi nazari a kan batutuwa takwas da shugaban kasa zai mayar da hankali a kansu, wato abubuwa takwas da za mu saka a gaba wajen ciyar da tattalin arzikin Nijeriya gaba wadanda suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samun jari, musamman wajen samar da bashi, hada kai ta kowane fanni, musamman matasa da mata, inganta tsaro, inganta wuraren zuba jari, bin doka da oda da kuma

yaki da cin hanci da rashawa.Wannan shi ne ainihin abin da tattaunawar ta kasance.”

Edun ya ce gwamnatin Tinubu ta gamu da mummunan yanayin tattalin arziki tare da hauhawar farashin kayayyaki na kashi 24 cikin 100 da kuma matsanancin rashin.

Tun da farko a wajen kaddamar da taron majalisar zartarwar, Tinubu ya hori ministocin da su duba girman mukamin da ofisoshinsu tare da mayar da hankali kan ayyukan da ke gabansu domin kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Next Post

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.