• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Takwas Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bai Wa Fifiko

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana abubuwa guda takwas da gwamnatinsa za ta fi bai wa fifiko wajen bunkasa tattalin arziki da zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ministan Kudi kuma ministan da ke kula da harkokin tattalin arziki, Wale Edun, ya gabatar da tsarin taswirar tattalin arziki, wanda aka yi la’akari da shi a farkon babban taron majalisar zartarwa ta tarayya da ya gudana a wannan mako.

  • Ranar Litinin Za A Kaddamar Da Jirgin Kasan Legas Da Zai Rika Jigilar Fasinja 175,000
  • Sin Na Shirin Sabunta Dabarun Kare Mabambantan Halittu Na Kasa Da Tsare-tsare

Edun wanda ya bayyana wa manema labarai na gidan gwamnati ajandar da suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, damar samun babban jari, inganta tsaro, inganta filin wasan da mutane da kamfanoni za su yi aiki, inganta tsarin dokokin kasa, da yaki da cin hanci da rashawa.

Ya ce majalisar zartarwa ta yi nazari a kan abubuwa takwas da suka fi ba da fifiko tare da gano abubuwan da za a cimma a cikin shekaru uku masu zuwa.

Edun ya ce shugaban kasa ya bai wa ministoci umurnin kan su fitar da manufofi da shirye-shirye a cikin makonni don inganta tattalin arzikin kasa tare da kyautata al’amura ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Edun ya ce majalisar ta amince da cewa tattalin arzikin bai kai inda ya kamata ba.

Game da batun alkiblar majalisar zantarwar ta dosa kuwa, ministan ya ce, “Tun da farko Shugaba Tinubu ya taya kowa murna tare da jaddada babban abin da ‘yan Nijeriya suke bukata, sannan ya karfafa muna gwiwa wajen jajircewa da kuma gudanar da yin aiki cikin gaggawa wajen samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Tun da farko, mun gudanar da wani atisaye na duba inda al’amura suka tsaya dangane da tattalin arziki, hauhawar farashin kayayyaki, hauhawar farashin kudadin waje, rashin aikin yi da sauransu.

“Babban abin da ya dace shi ne, ba inda ya kamata mu kasance ba, mun kuma yi nazari a kan batutuwa takwas da shugaban kasa zai mayar da hankali a kansu, wato abubuwa takwas da za mu saka a gaba wajen ciyar da tattalin arzikin Nijeriya gaba wadanda suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samun jari, musamman wajen samar da bashi, hada kai ta kowane fanni, musamman matasa da mata, inganta tsaro, inganta wuraren zuba jari, bin doka da oda da kuma

yaki da cin hanci da rashawa.Wannan shi ne ainihin abin da tattaunawar ta kasance.”

Edun ya ce gwamnatin Tinubu ta gamu da mummunan yanayin tattalin arziki tare da hauhawar farashin kayayyaki na kashi 24 cikin 100 da kuma matsanancin rashin.

Tun da farko a wajen kaddamar da taron majalisar zartarwar, Tinubu ya hori ministocin da su duba girman mukamin da ofisoshinsu tare da mayar da hankali kan ayyukan da ke gabansu domin kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Next Post

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

LABARAI MASU NASABA

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.