• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Takwas Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Bai Wa Fifiko

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana abubuwa guda takwas da gwamnatinsa za ta fi bai wa fifiko wajen bunkasa tattalin arziki da zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Ministan Kudi kuma ministan da ke kula da harkokin tattalin arziki, Wale Edun, ya gabatar da tsarin taswirar tattalin arziki, wanda aka yi la’akari da shi a farkon babban taron majalisar zartarwa ta tarayya da ya gudana a wannan mako.

  • Ranar Litinin Za A Kaddamar Da Jirgin Kasan Legas Da Zai Rika Jigilar Fasinja 175,000
  • Sin Na Shirin Sabunta Dabarun Kare Mabambantan Halittu Na Kasa Da Tsare-tsare

Edun wanda ya bayyana wa manema labarai na gidan gwamnati ajandar da suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, damar samun babban jari, inganta tsaro, inganta filin wasan da mutane da kamfanoni za su yi aiki, inganta tsarin dokokin kasa, da yaki da cin hanci da rashawa.

Ya ce majalisar zartarwa ta yi nazari a kan abubuwa takwas da suka fi ba da fifiko tare da gano abubuwan da za a cimma a cikin shekaru uku masu zuwa.

Edun ya ce shugaban kasa ya bai wa ministoci umurnin kan su fitar da manufofi da shirye-shirye a cikin makonni don inganta tattalin arzikin kasa tare da kyautata al’amura ga dukkan ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Edun ya ce majalisar ta amince da cewa tattalin arzikin bai kai inda ya kamata ba.

Game da batun alkiblar majalisar zantarwar ta dosa kuwa, ministan ya ce, “Tun da farko Shugaba Tinubu ya taya kowa murna tare da jaddada babban abin da ‘yan Nijeriya suke bukata, sannan ya karfafa muna gwiwa wajen jajircewa da kuma gudanar da yin aiki cikin gaggawa wajen samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya. Tun da farko, mun gudanar da wani atisaye na duba inda al’amura suka tsaya dangane da tattalin arziki, hauhawar farashin kayayyaki, hauhawar farashin kudadin waje, rashin aikin yi da sauransu.

“Babban abin da ya dace shi ne, ba inda ya kamata mu kasance ba, mun kuma yi nazari a kan batutuwa takwas da shugaban kasa zai mayar da hankali a kansu, wato abubuwa takwas da za mu saka a gaba wajen ciyar da tattalin arzikin Nijeriya gaba wadanda suka hada da samar da abinci, kawo karshen talauci, bunkasar tattalin arziki da samar da ayyukan yi, samun jari, musamman wajen samar da bashi, hada kai ta kowane fanni, musamman matasa da mata, inganta tsaro, inganta wuraren zuba jari, bin doka da oda da kuma

yaki da cin hanci da rashawa.Wannan shi ne ainihin abin da tattaunawar ta kasance.”

Edun ya ce gwamnatin Tinubu ta gamu da mummunan yanayin tattalin arziki tare da hauhawar farashin kayayyaki na kashi 24 cikin 100 da kuma matsanancin rashin.

Tun da farko a wajen kaddamar da taron majalisar zartarwar, Tinubu ya hori ministocin da su duba girman mukamin da ofisoshinsu tare da mayar da hankali kan ayyukan da ke gabansu domin kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Adalci, Amana, Kamewa Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Next Post

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

2 hours ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 week ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Tinubu
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

Da Goyon Bayanku Zamu Lashe Firimiyar Nijeriya —Kyaftin Din Katsina United 

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.