• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh

by Sani Anwar
1 year ago
in Labarai
0
Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ‘yan Nijeriya ke ci gaba da kokawa a kan rashin saukar farashin kayayyaki, Shugaban Gamayyar Kungiyoyin Tabbatar da Zaman Lafiya da Wayar da Kai ta Kasa (NACOPEAM), Dakta Ahmad Saleh, ya bayyana hanyoyin da za a bi; don warware matsalar hauhuwar farashin kaya a Nijeriya.

Saleh ya bayyana abubuwan ne a shirin Barka Da Hantsi Nijeriya na Sashen Talabijin na Intanet na LEADERSHIP Hausa, da aka gabatar ranar Larabar da ta gabata.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo

Dakta Saleh, ya nunar da cewa matukar ana so a cimma burin haka, da farko ya kamata a kafa Hukumar Kayyade Farashi a Nijeriya.

“Idan ana so farashin kaya ya sauka a wannan kasa, wajibi ne a kafa wannan hukuma; wadda za ta yi aiki a lungu da sako na wannan kasa baki-daya.”

Kamar yadda Daktan ya bayyana a shirin, ya ce kafa wannan hukuma zai taimaka wajen kayyade farashin kayayyaki, inda ya bayar da misali da cewa ana sayar da Simintin Dangode a kan dubu shida da wani abu a Legas amma a Mambila Naira dubu tara ake sayarwa kuma a cikin kasa daya wanda haka bai kamata ba.

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Haka zalika, dole ne wannan hukuma ta tabbatar da samar da farashin bai-daya a dukkanin kananan hukumomi 774 da muke da su a Nijeriya. “Wannan na daya daga cikin abubuwan da za su taimakawa wajen saukar farashin kayayyakin da ke ci wa ‘yan Nijeriya tiwo a kwarya a daidai wannan lokaci.” Ya bayyana.

Abu na biyu, kamar yadda Dr. Saleh ya bayyana shi ne, Bunkasa Masana’antun Cikin Gida: Bunkasa masana’antu zai taimaka kwarai da gaske wajen saukar farashin kayayyaki a cewar Masanin, domin kuwa a duk yayin da ya kasance abubuwan da ake shigowa da su; sun rinjayi wadanda ake fita da su, dole ne a fuskanci matsalar hauhawar farashin kaya.

Ya kara da cewa, wajibi ne gwamnati ta mayar da hankali wajen farfado da masana’antu tare da karfafa samar da abubuwan da za a rika fitar da su zuwa kasashen ketare, don sake farfado da tattalin arzikin wannan kasa, misali kamar bangaren harkar noma, ma’adanai da sauran makamantansu.

Domin kuwa, Nijeriya kasa ce da Allah ya azurta da dukkanin wani nau’i na arziki, wanda idan aka tsaya aka kyautata amfani da shi yadda ya kamata, za a samu kyautatuwar tattalin arziki da wadata da kuma jin dadi a kasar baki-daya.

Sai kuma na uku, da ya yi kiran a kafa Kotun Hukunta Duk Wanda Ya Bijire Wa Dokar Kasa: “Idan har ana so a cimma wannan manufa ta samun saukar farashin kayayyaki a fadin wannan kasa, ya zama wajibi ya kasance ana hukunta duk wanda ya ci karo da doka. Misali, a Kasar Ghana, lokacin da bankuna suka saba wa ka’idojin harkokin kudaden waje; ba tare da wani bata lokaci ba aka hukunta su”, in ji Daktan.

Don haka, ya zama dole Nijeriya ta mike tsaye wajen hukunta masu aikata laifuka, musamman ma wadanda aka samu da laifin cin hanci da rashawa, ya kasance ana yanke musu hukunci irin na babu sani; babu sabo. Dalili kuwa, babu abin da ya mayar da Nijeriya baya tare da dakile ci gabanta, kamar wannan dambarwa ta cin hanci da rashawa a wannan kasa, a cewar Dakta Sale.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FarashiKayayyakiSauki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Shirin Auren Zawarawan Kano A Sikeli

Next Post

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

5 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

19 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

21 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

24 hours ago
Next Post
Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.