ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bankuna Da Cibiyoyin Kudi Ke Tafka Asara Sakamakon Fara Amfani Da Fasahar Zamani Ta AI

by Bello Hamza
2 years ago
AI

Da sannu a hankali fasahar zamani na Artificial Interligent na neman mamaye yadda bankuna da cibiyoyin kudi ke gudanar da harkokinsu, a kan haka ‘yan Nijeriya da masana ke bayyana tsoron su na yiwuwar karuwar harkokin ‘yan damfara da cuwacuwa saboda dogaro da wannan fasahar, masu hulda da bankuna da bankunan su kansu za su ci gaba da tafka asarar makudan kudade kamar yadda binciken jaridar LEADERSHIP ya nuna.

Wannan na faruwa ne a daidai lokacin da Nijeriya ke asarar dala miliyan 500 sakamakonm sata ta intanet, wanda hakan ke nuna kudin ya kai Naira biliyan 675 a duk shekara inda ka yi amfani da canjin naira 1,350 a kan dala 1.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Da Ɗumi-ɗumi: EFCC Za Ta Gurfanar Da Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama Da ‘Yarsa A Gobe Alhamis

Kididdga daga hukumar sadarwar Nijeriya NCC ya nuna cewa, Nijeriya na asarar kudaden da aka ambata ne a bangarori daban-daban yayin da bangaren bankunan Nijeriya ya yi asarar fiye da Dala biliyan 8 ga ayyukan masu zamba ta intane a shekarar 2022 kawai.

ADVERTISEMENT

Hukumar sadarwar ta bayyana cewa, kashi 71 kawai ne bankuna ke bayar da rahoton harin da ake kai musu ta intanet, amma hukumar kula da harkokin bankuna a Nijeriya ‘Nigeria Interbank Bank Settlement System (NIBSS), ta sanar da cewa, bangaren bankuna a Nijeriya sun yi asarar fiye da naira biliyan 50.5 ga masu zamba ta intanet a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2023.

Fasahar zamani na musamman da ake kira da ‘Artificial Intelligence (AI)’ fasaha ce da ake tafiyar da harkoki tamkar irin na dan adam, an shirya na’ura ta yadda za ta rinka aikin yau da kullum na banki tamkar dan adam kuma a cikin sauri.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Duk da cewa, wannan fasahar ta AI abu ne mai kyau ga bangaren bankuna, inshora da sauran harkokin kudi amma matsalar ita ce yadda za a kare bayanai da kuma sirrukan masu hulda.

Babban damuwar al’umma anan shi ne yadda wasu bayanai na sirri na al’umma da za a iya sanya wa fasahar AI za su iya fadawa hannun bata gari ta yadda za su iya amfani da su wajen damfarar masu hulda da wadnnan cibiyoyin kudi, ba tare da sun sani ba.

A kan haka aka gargadi ‘yan Nijeriya da su yi hattara da irin manhajojin AI da suke saukewa a wayoyinsu don su kan kasance wasu kafa na lekan asiri da bata gari ke amfani da su wajen satar bayanai masu muhimmanci daga wayoyin mutane domin aikata muggan ayyukansu na damfara.

Hukumar Lamuni ta Duniya IMF, ta bayyana cewa, cibiyoyin kudi sun sanar da asarar kudaden da ya kai dala biliyan 12 tun daga shekarar 2004 da kuma asarar dala biliyan 2.5 tun daga shekarar 2020.

A rahotonta na halin da bangaren harkar kudi na duniya yake tafiya na shekarar 2024, IMF ta bayyana cewa, hare-hare ta intanet ga bankuna yana kara karuwa a kullum, inda ake asarar kudade masu dimbin yawa.

Masana sun bayyana cewa, masu aikata laifi ta inatne sun rungumi tsarin AI, inda suka fito da sabbin dabaru na rudar da mutane inda suke amfani da jimloli masu tsawo waje aikata damfara musamman ga bankuna a fadin duniya.

A yayin da ake ci gaba sauraron aukuwar karin hare-haren na ‘yan damfara masu amfani da AI, masana sun bayar da shawarar, a karfafa dabarun kariya ga manhajojin bankuna masu AI tare da kuma sabunta su aka-akai.

Rahoto na baya-bayan nan daga cibiyar binciken laifukkan da ake aikatawa da kwamfuta, ‘Computer Crime Research Centre (CCRC)’ ta yi lura da cewa, damfara ta intanet ya haura zuwa akalla dala tiriliyan 12 a shekrar 2024 saboda amfani da fasahar AI, rahoton ya kara da cewa, “A shekarun 2024 da 2025, za mu fuskanci karuwar ayyukan ‘yan damfara ta intanet masu kai hari ga bankuna, za kuma mu ga karuwar amfani da fasahar AI wajen aitaka wadanna ayyukan rashin gaskiyar.

“Fasahar Deepfake zai mamaye tsofaffin hanyoyin da ‘yan damfara ke amfani dasu. Yayin da harkokin kasuwanci da dama za su rungumi fasahar AI, za kuma su fuskanci gaggarumar barazana daga masu aikata laifukka ta intanet musamman amfani da fasahar AI, wadanda za su bullo da sabbin fasahohi da za su karya duk wata kariya da cibiyoyin kudin ke samarwa.

“Bangaren da za su fi fadawa wannan hadarin sun hada da masu kananan kasuwanci da cibiyoyin kudi da basu da manyan jari wadanda ba za su iya saye tare da samar wa kan su manhajoji masu karfi da za su bayar da kariyar da ake bukata ba,” in ji rahoton.

Da yake tabbatar da sakamakon wannan rahoton, wani tsohon darakta a hukumar NDIC, Dakta Jacob Afolabi, ya lura da cewa, an samu karuwar hare-hare ga cibiyoyin kudi ta hanyar fasahar AI a shekarar 2023, sun kuma aukar da gaggarumin asara ga cibiyoyi da hukumomin gwamnati.

Afolabi ya kuma yi bayanin cewa, fasahar AI na iya sarrafa bayanai masu yawan gaske a lokaci daya, abin da yake kara tsoron kariya ga sirrin wadanan bayanai da kuma tsaronsu.

“Fasahar Al na kara karuwa tare da sarkakiya, haka kuma kare masu amfani da su yake kara wahala ga kuma yiwuwar an yi amfani da su ta barauniyar hanya yana kara karuwa. Masu aikata laifukka ta intanet na kara fito da sabbin hanyoyin da za su karya duk wata kariya da aka yi wa fasahar AI don su cutar da masu amfani da ita musamman a bangaren cibiyoyin kudi da sauransu,” in ji shi.

Domin samar da kariya ga bayanan al’umma, Afolabi ya bayar da shawarar a samar da dokoki na musamman domin kariya ga masu amfani da fasahar AI.

Dogaro kacikan ga fasahar AI yana kaiwa ga rasa zimma daga nutane, tunani mai amfani da kuma rasa hannun dan adama abin da ake yi, a kan haka tsohon daraktan ya bayar da shawarar cewa, ya kamata a samar da daidaito a tsakanin amfani da fasahar AI da kuma amfani da dan adama a harkokin bankuna da wuraren da ake amfani da fasahar AI saboda samar da kariya da kuma sanya ido na dan adam a harkokin yau da kullum.

Ya kuma kara da cewa, “rungumar fasahar AI na iya haifar da rasa ayyukan yi ga al’umma a ma’aikatu musamman ga ma’aikatan da basu da kwarewa na musamman, dole ma’aikata su rungumi ilimin fasahar zamani in har suna son kasancewa a fagen ayyuka a wannan zamani,”.

Haka kuma darakta mai kula harkokin gwamnati a kamfanin Microsoft Africa, Akua Gyekye, ya ce in har ana son amfani da fasahar AI a cikin nasara dole hukumomin gwamnati su rungumi tsarin tare da samar da tsarin gudanar da ayyukan a hukumance.

Ya bayyana cewa, kasashen Afrika da dama sun fara samar da dokoki da tsare-tsare a hukumance a kan tafiyar da fasahar AI, hakan ya kuma kai ga shirye-shiryen samar da wani tsari da zai tafiyar da hanyoyin kariya ga fasahar AI a duniya gaba daya.

Ta kuma kara da cewa, Kungiyar Tarayyar Afrika ta kira taron masana kimiyyar sadarwa a wannan shekarar inda suka samar da daftarin dokoki na yadda za a tafiyar da harkokin fasahar AI a tsakanin kasashen Afrika.

Wani jami’i a hukumar sadarwa ta Nijeriya NCC, Kelechi Nwankwo, ya ce, duk da bunkasar harkokin sadarwar zamani a Nijeriya, ana fuskantar hare-hare na intanet abin kuma na iya karuwa a nan gaba.

Da yake nuna damuwarsa, shugaban kamfanin inshora na Guinea Insurance Plc, Ademola Abidogun, ya ce, duk da cewa, amfani da fasahar AI na da muhimmanci ga bangaren inshora amma matsalolin da ke tattare da hakan suna da yawan gaske, musamman a bangaren kariya ga bayanai na sirri na al’umma.

Tun da farko hukumar Lamuni ta Duniya IMF ta bayyana cewa, masu aikata laifi ta intanet sune babbar barazana ga harkokin cibiyoyin kudi inda suke dagula harkokin bankuna suna kuma sanya tsoro ga masu hulda da cibiyoyin kudin gaba daya.

Domin karfafa bangaren bankuna da cibiyoyin kudin, IMF ta bayar da shawara ga manyan bankuna kasa na su samar da tsarin kasa na yaki da masu zamba ta intanet tare da sanya ido da kuma aiwatar da dukkan dokokin da aka samar na kariya daga sharrin masu aikata zamba ta intanet.

Haka kuma, a nasa tsokacin, shgaban kungiyar jami’an kula da tsaron bankuna a Nijeriya (CCISONFI), Mr. Festus Amede, ya bayyana bukatar samar da tsarin kariya ga bayanan sirri a cibiyoyin kudin kasar nan musamman daga barazanar masu aikata laifi ta intanet.

AI
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.