• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Zan Yi Idan Aka Zabe Ni – Tinubu 

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Abubuwa Uku Da Zan Yi Idan Aka Zabe Ni – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin inganta tsaro, sauya tattalin arziki da sauransu, yayin da ya bayyana abubuwa uku da zai yi idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekara mai zuwa. 

Ya tabbatar wa shugaban kasa, Muhammadu Buhari kudirinsa na girmama kokarinsa da abubuwan da ya bari bayan wa’adinsa a 2023.

  • PDP Ta Zargi Makiyan Dimokuradiyya Da Kitsa Hargitsi A Gangamin Da Jam’iyyar Ta Yi A Kaduna
  • Rundunar Soji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6 A Borno

Tsohon gwamnan na Jihar Legas ya yi wadannan alkawuran ne a lokacin da ya gabatar da sakon fatan alheri a taron kwana uku na ministoci da sakatarorin dindindin da ke gudana a Abuja a ranar Talata.

Ya kuma yaba wa gwamnatin Buhari bisa yadda ta samar da mulki mai tsari ga kasar nan, inda ya bayyana cewa shugaban ya dora kasar nan a kan turba mai kyau bayan shekaru da dama da aka shafe ana fama da rashin adalci.

Tinubu ya ce zai yi sa’a, idan aka zabe shi, ya karbi ragamar mulki daga gwamnatin da ta taka rawar gani sosai, inda ya yi alkawarin dora wa daga inda gwamnatin Buhari ta tsaya.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

“Ku tabbatar da cewa an rubuta tarihin zamanin Buhari daidai, domin ta hada tubalan ginin don dorewar makoma ta wadata, zaman lafiya, ci gaba iri-iri da tsaro.

“Saboda haka, ina farin ciki da aka ba ni sandar gadon shugaba Buhari a matsayin mai rike da madafun iko a jam’iyyarmu, kuma ina fatan a matsayina na dan takarar shugaban kasarmu.

“Shugaban kasa da membobin gwamnatinsa, bari in bayyana kamar haka: Idan aka zabe ni, zan ba da girmamawar da ta dace ga kokarinku da abin da kuka bari.

“Zan yi aiki cikin kyakkyawan hadin kai da manufar kasa wacce ta samar da kafa jam’iyyarmu tare da bayyana ayyukan gwamnatinku.

“Mafi muhimmanci, hanyoyin da gwamnatin Tinubu za su himmatu don kara kariya da wadata al’ummar Nijeriya saboda manufarmu ita ce samar da kyakkyawan tsarin gudanar da mulki da gyara ga kasarmu.

Da yake magana a kan taken, “Habaka Tsaro, Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Sauya Tattalin Arziki’, Tinubu ya bayyana farin cikinsa da kasancewa daya daga cikin magoya bayan gwamnatin tun daga rana ta daya.

Ya yaba wa Buhari da majalisarsa kan rashin bai wa ‘yan Nijeriya kunya da suka yi imani da su.

“Na gode shugaba Buhari, a madadin daukacin ‘yan Nijeriya da daukacin gwamnatinka, da wanda duk ya halarci taron nan a yau ko ya wakilta, mun ba ka goyon baya tun daga ranar farko da ka hau mulki, zan ci gaba da kasancewa amininka kuma ko da bayan ka sauka.

“Na san irin hangen nesan da kuka yi wa Nijeriya. Na san irin sadaukarwar da kuka yi wa wannan al’umma. Na san abubuwan da kuka cimma.

“Zan iya fada muku cewar abubuwan da kuka yi suna da muhimmanci kuma masu dorewa ne,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Abubuwa 3AlkawuraAPCtakaraTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bukaci A Sanya Dokar Ta Baci Kan Harkar Ilimi A Matakin Farko

Next Post

Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa ‘Yan Bindiga A Jihar Zamfara

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

2 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

6 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

7 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Gargaɗi Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa ‘Yan Bindiga A Jihar Zamfara

Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa 'Yan Bindiga A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.