• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Zan Yi Idan Aka Zabe Ni – Tinubu 

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
Abubuwa Uku Da Zan Yi Idan Aka Zabe Ni – Tinubu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin inganta tsaro, sauya tattalin arziki da sauransu, yayin da ya bayyana abubuwa uku da zai yi idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekara mai zuwa. 

Ya tabbatar wa shugaban kasa, Muhammadu Buhari kudirinsa na girmama kokarinsa da abubuwan da ya bari bayan wa’adinsa a 2023.

  • PDP Ta Zargi Makiyan Dimokuradiyya Da Kitsa Hargitsi A Gangamin Da Jam’iyyar Ta Yi A Kaduna
  • Rundunar Soji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6 A Borno

Tsohon gwamnan na Jihar Legas ya yi wadannan alkawuran ne a lokacin da ya gabatar da sakon fatan alheri a taron kwana uku na ministoci da sakatarorin dindindin da ke gudana a Abuja a ranar Talata.

Ya kuma yaba wa gwamnatin Buhari bisa yadda ta samar da mulki mai tsari ga kasar nan, inda ya bayyana cewa shugaban ya dora kasar nan a kan turba mai kyau bayan shekaru da dama da aka shafe ana fama da rashin adalci.

Tinubu ya ce zai yi sa’a, idan aka zabe shi, ya karbi ragamar mulki daga gwamnatin da ta taka rawar gani sosai, inda ya yi alkawarin dora wa daga inda gwamnatin Buhari ta tsaya.

Labarai Masu Nasaba

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

“Ku tabbatar da cewa an rubuta tarihin zamanin Buhari daidai, domin ta hada tubalan ginin don dorewar makoma ta wadata, zaman lafiya, ci gaba iri-iri da tsaro.

“Saboda haka, ina farin ciki da aka ba ni sandar gadon shugaba Buhari a matsayin mai rike da madafun iko a jam’iyyarmu, kuma ina fatan a matsayina na dan takarar shugaban kasarmu.

“Shugaban kasa da membobin gwamnatinsa, bari in bayyana kamar haka: Idan aka zabe ni, zan ba da girmamawar da ta dace ga kokarinku da abin da kuka bari.

“Zan yi aiki cikin kyakkyawan hadin kai da manufar kasa wacce ta samar da kafa jam’iyyarmu tare da bayyana ayyukan gwamnatinku.

“Mafi muhimmanci, hanyoyin da gwamnatin Tinubu za su himmatu don kara kariya da wadata al’ummar Nijeriya saboda manufarmu ita ce samar da kyakkyawan tsarin gudanar da mulki da gyara ga kasarmu.

Da yake magana a kan taken, “Habaka Tsaro, Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Sauya Tattalin Arziki’, Tinubu ya bayyana farin cikinsa da kasancewa daya daga cikin magoya bayan gwamnatin tun daga rana ta daya.

Ya yaba wa Buhari da majalisarsa kan rashin bai wa ‘yan Nijeriya kunya da suka yi imani da su.

“Na gode shugaba Buhari, a madadin daukacin ‘yan Nijeriya da daukacin gwamnatinka, da wanda duk ya halarci taron nan a yau ko ya wakilta, mun ba ka goyon baya tun daga ranar farko da ka hau mulki, zan ci gaba da kasancewa amininka kuma ko da bayan ka sauka.

“Na san irin hangen nesan da kuka yi wa Nijeriya. Na san irin sadaukarwar da kuka yi wa wannan al’umma. Na san abubuwan da kuka cimma.

“Zan iya fada muku cewar abubuwan da kuka yi suna da muhimmanci kuma masu dorewa ne,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Abubuwa 3AlkawuraAPCtakaraTinubuZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bukaci A Sanya Dokar Ta Baci Kan Harkar Ilimi A Matakin Farko

Next Post

Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa ‘Yan Bindiga A Jihar Zamfara

Related

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

1 day ago
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

2 days ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

5 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

5 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

6 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

6 days ago
Next Post
Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa ‘Yan Bindiga A Jihar Zamfara

Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa 'Yan Bindiga A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.