ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwa Uku Da Zan Yi Idan Aka Zabe Ni – Tinubu 

by Sadiq
4 years ago
Tinubu

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi alkawarin inganta tsaro, sauya tattalin arziki da sauransu, yayin da ya bayyana abubuwa uku da zai yi idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa a shekara mai zuwa. 

Ya tabbatar wa shugaban kasa, Muhammadu Buhari kudirinsa na girmama kokarinsa da abubuwan da ya bari bayan wa’adinsa a 2023.

  • PDP Ta Zargi Makiyan Dimokuradiyya Da Kitsa Hargitsi A Gangamin Da Jam’iyyar Ta Yi A Kaduna
  • Rundunar Soji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6 A Borno

Tsohon gwamnan na Jihar Legas ya yi wadannan alkawuran ne a lokacin da ya gabatar da sakon fatan alheri a taron kwana uku na ministoci da sakatarorin dindindin da ke gudana a Abuja a ranar Talata.

ADVERTISEMENT

Ya kuma yaba wa gwamnatin Buhari bisa yadda ta samar da mulki mai tsari ga kasar nan, inda ya bayyana cewa shugaban ya dora kasar nan a kan turba mai kyau bayan shekaru da dama da aka shafe ana fama da rashin adalci.

Tinubu ya ce zai yi sa’a, idan aka zabe shi, ya karbi ragamar mulki daga gwamnatin da ta taka rawar gani sosai, inda ya yi alkawarin dora wa daga inda gwamnatin Buhari ta tsaya.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Ku tabbatar da cewa an rubuta tarihin zamanin Buhari daidai, domin ta hada tubalan ginin don dorewar makoma ta wadata, zaman lafiya, ci gaba iri-iri da tsaro.

“Saboda haka, ina farin ciki da aka ba ni sandar gadon shugaba Buhari a matsayin mai rike da madafun iko a jam’iyyarmu, kuma ina fatan a matsayina na dan takarar shugaban kasarmu.

“Shugaban kasa da membobin gwamnatinsa, bari in bayyana kamar haka: Idan aka zabe ni, zan ba da girmamawar da ta dace ga kokarinku da abin da kuka bari.

“Zan yi aiki cikin kyakkyawan hadin kai da manufar kasa wacce ta samar da kafa jam’iyyarmu tare da bayyana ayyukan gwamnatinku.

“Mafi muhimmanci, hanyoyin da gwamnatin Tinubu za su himmatu don kara kariya da wadata al’ummar Nijeriya saboda manufarmu ita ce samar da kyakkyawan tsarin gudanar da mulki da gyara ga kasarmu.

Da yake magana a kan taken, “Habaka Tsaro, Yaki da Cin Hanci da Rashawa, Sauya Tattalin Arziki’, Tinubu ya bayyana farin cikinsa da kasancewa daya daga cikin magoya bayan gwamnatin tun daga rana ta daya.

Ya yaba wa Buhari da majalisarsa kan rashin bai wa ‘yan Nijeriya kunya da suka yi imani da su.

“Na gode shugaba Buhari, a madadin daukacin ‘yan Nijeriya da daukacin gwamnatinka, da wanda duk ya halarci taron nan a yau ko ya wakilta, mun ba ka goyon baya tun daga ranar farko da ka hau mulki, zan ci gaba da kasancewa amininka kuma ko da bayan ka sauka.

“Na san irin hangen nesan da kuka yi wa Nijeriya. Na san irin sadaukarwar da kuka yi wa wannan al’umma. Na san abubuwan da kuka cimma.

“Zan iya fada muku cewar abubuwan da kuka yi suna da muhimmanci kuma masu dorewa ne,” in ji shi.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Tinubu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa ‘Yan Bindiga A Jihar Zamfara

Gwamnati Ta Kama Mutum 80 Da Zargin Taimakawa 'Yan Bindiga A Jihar Zamfara

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.