• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
in Ado Da Kwalliya
0
Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu alaikum masu karatu barkammu da sake haduwa da ku a wannan mako a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Ado da Kwalliya.

A yau shafin namu ya yo muku tsaraba ne da wani sirri da ke tattarai da Abarba wajen gyaran fata.

  • Gyaran Amarya Kafin Lokacin Aure
  • Gyaran Fatar Fuska

Za ku yi mamaki, babbar fa’idar Abarba da ake samu baya ga fa’idodin da take da su a bangaran inganta lafiyar jiki kamar shahararren sirrinta na narkar da abinci da kuma habaka rigakafi.

Abarba tana da matukar kyau da tasiri wajen inganta lafiyar jama’a gaba daya, amma baya ga haka abin da wannan kayan marmarin yake yi na musamman da yake da matukar mamaki shi ne abin da za mu zo da shi a rubutun namu na yau wanda yake da matukar kyau da amfani.

Wannan dan itace yana da isasshen sinadarin bitamin da sinadarin kara karfin kashi da sauran sinadarai irin su ‘Manganese’, ‘calcium’, ‘sodium’, da magnesium, wadannan duk suna cikin Abarba.

Labarai Masu Nasaba

Maganin Kurajen Fuska

Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?

Binciken masana kiwon lafiya da masana bangaran magungunan da abinci ke yi ga dan’Adam sun tabbatar da cewa Abarba tana habaka lafiyar fata idan aka sha ta yadda take ko ta hanyar shafa ruwanta a-kai-a-kai. Ga sauran wasu sirrukan abin da Abarba ke yi ga dan’Adam:

Yaki da tsufa

Akwai mata da dama wadanda suke da shekaru a duniya amma sun tsani a rika yi musu kallon tsofaffi, to ina ire-iren wadannan matan, hanya mafi sauki da za ku rika yakar tsufanku ita ce ku rika shan Abarba a-kai-a-kai. Lallai bincike ya tabbatar da Abarba tana jinkirta saurin tsufa saboda sinadaran da take dauke da su na yaki da yamutsewar fata.

Tana rage duhu ko tabon baki a jiki

Abarba tana dauke da wadataccen sindarin ‘Ascorbric Acid’ wadda yake matukar taimakawa wajen yaki da tabon ciwo da ya yi baki a jiki. Haka nan idan kina son kawar da bakin da ba ki so a wata gaba ta jikinki, kawai ki shafa ruwan Abarba a kan wuraren da suke da duhun, ki barshi na tsawon mintuna biyar, sannan ki wanke da ruwan dumi, za ki sha mamaki cikin yardar Allah.

 Barkewar kurajen fuska:

Har ila yau, wani sirri da Abarba take dauke da shi shi ne, kawar da kuraje masu sa duhu a fuska, ana ba da shawarar cewa idan mace tana son hana wadannan kurajen na fuska su bata mata kyan fuska ta rika shafa ruwan Abarba za ta samu za ta sha mamaki.

Gyara fata

Abarba tana kunshe da sinadaran ‘Enzymes’ wanda ke cire matattun kwayoyin halittar fata da kuma haskaka fata. Don haka, idan kina so fatarki ta kara haske (ba irin na bilicin ba), ki rungumi sha da shafa Abarba.

Tana taimaka wa warkar da raunuka.

Abarba tana da wani sinadari maganin ‘Antiodidant’, da na bitamin C wadanda suke iya taimakawa wajen hana lalacewar kwayoyin fata. Don haka idan aka yi amfani da ita tana iya taimakawa wajen saurin warkar da rauni ta hanyar tallafa wa samar da sabbin kwayoyin fata.

Ina fata mun amfana da wannan tsaraba. Sai kuma mako mai zuwa idan Allah ya kai mu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Za Ta Fadada Girman Tashar Binciken Samaniyarta

Next Post

Kisan Sojojin Kasar Nijar 29 Ya Ja Hankalin Shugabannin Afirka

Related

Maganin Kurajen Fuska
Ado Da Kwalliya

Maganin Kurajen Fuska

2 weeks ago
Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?
Ado Da Kwalliya

Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?

3 weeks ago
Maganin Karin Kiba
Ado Da Kwalliya

Maganin Karin Kiba

4 weeks ago
Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)
Ado Da Kwalliya

Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

1 month ago
Hanyoyin Warware Matsalolin Ma’aurata(1)
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Warware Matsalolin Ma’aurata(1)

1 month ago
Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)
Ado Da Kwalliya

Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

1 month ago
Next Post
Kisan Sojojin Kasar Nijar 29 Ya Ja Hankalin Shugabannin Afirka

Kisan Sojojin Kasar Nijar 29 Ya Ja Hankalin Shugabannin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.