ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Al’ajabi Da Abarba Ke Yi Wajen Gyaran Fata

by Bilkisu Tijjani
3 years ago
Abarba

Assalamu alaikum masu karatu barkammu da sake haduwa da ku a wannan mako a cikin shirin namu mai farin jini da albarka na Ado da Kwalliya.

A yau shafin namu ya yo muku tsaraba ne da wani sirri da ke tattarai da Abarba wajen gyaran fata.

  • Gyaran Amarya Kafin Lokacin Aure
  • Gyaran Fatar Fuska

Za ku yi mamaki, babbar fa’idar Abarba da ake samu baya ga fa’idodin da take da su a bangaran inganta lafiyar jiki kamar shahararren sirrinta na narkar da abinci da kuma habaka rigakafi.

ADVERTISEMENT

Abarba tana da matukar kyau da tasiri wajen inganta lafiyar jama’a gaba daya, amma baya ga haka abin da wannan kayan marmarin yake yi na musamman da yake da matukar mamaki shi ne abin da za mu zo da shi a rubutun namu na yau wanda yake da matukar kyau da amfani.

Wannan dan itace yana da isasshen sinadarin bitamin da sinadarin kara karfin kashi da sauran sinadarai irin su ‘Manganese’, ‘calcium’, ‘sodium’, da magnesium, wadannan duk suna cikin Abarba.

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

Binciken masana kiwon lafiya da masana bangaran magungunan da abinci ke yi ga dan’Adam sun tabbatar da cewa Abarba tana habaka lafiyar fata idan aka sha ta yadda take ko ta hanyar shafa ruwanta a-kai-a-kai. Ga sauran wasu sirrukan abin da Abarba ke yi ga dan’Adam:

Yaki da tsufa

Akwai mata da dama wadanda suke da shekaru a duniya amma sun tsani a rika yi musu kallon tsofaffi, to ina ire-iren wadannan matan, hanya mafi sauki da za ku rika yakar tsufanku ita ce ku rika shan Abarba a-kai-a-kai. Lallai bincike ya tabbatar da Abarba tana jinkirta saurin tsufa saboda sinadaran da take dauke da su na yaki da yamutsewar fata.

Tana rage duhu ko tabon baki a jiki

Abarba tana dauke da wadataccen sindarin ‘Ascorbric Acid’ wadda yake matukar taimakawa wajen yaki da tabon ciwo da ya yi baki a jiki. Haka nan idan kina son kawar da bakin da ba ki so a wata gaba ta jikinki, kawai ki shafa ruwan Abarba a kan wuraren da suke da duhun, ki barshi na tsawon mintuna biyar, sannan ki wanke da ruwan dumi, za ki sha mamaki cikin yardar Allah.

 Barkewar kurajen fuska:

Har ila yau, wani sirri da Abarba take dauke da shi shi ne, kawar da kuraje masu sa duhu a fuska, ana ba da shawarar cewa idan mace tana son hana wadannan kurajen na fuska su bata mata kyan fuska ta rika shafa ruwan Abarba za ta samu za ta sha mamaki.

Gyara fata

Abarba tana kunshe da sinadaran ‘Enzymes’ wanda ke cire matattun kwayoyin halittar fata da kuma haskaka fata. Don haka, idan kina so fatarki ta kara haske (ba irin na bilicin ba), ki rungumi sha da shafa Abarba.

Tana taimaka wa warkar da raunuka.

Abarba tana da wani sinadari maganin ‘Antiodidant’, da na bitamin C wadanda suke iya taimakawa wajen hana lalacewar kwayoyin fata. Don haka idan aka yi amfani da ita tana iya taimakawa wajen saurin warkar da rauni ta hanyar tallafa wa samar da sabbin kwayoyin fata.

Ina fata mun amfana da wannan tsaraba. Sai kuma mako mai zuwa idan Allah ya kai mu.

Abarba
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi
Ado Da Kwalliya

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa
Ado Da Kwalliya

A Matsayinki Na Mace, Kada Ki Yi Wasa Da Wadannan Abubuwa

June 6, 2026
Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?
Ado Da Kwalliya

Ko Kin San… Cututtukan Da Man Ridi Ke Warkarwa?

May 17, 2026
Next Post
Kisan Sojojin Kasar Nijar 29 Ya Ja Hankalin Shugabannin Afirka

Kisan Sojojin Kasar Nijar 29 Ya Ja Hankalin Shugabannin Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.