Ministan Babban Birnin Tarayya, (FCT), Nyesom Wike, ya sha alwashin magance gibin ababen more rayuwa a Abuja.
Ministan ya bayyana cewa ta fuskar samar da ababen more rayuwa, babban birnin tarayya za ta zama wani abu daban lokacin da gwamnatin Bola Tinubu ta kare wa’adinta na farko a shekarar 2027.
- Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
- CMSA: An Yi Nasarar Harba Kumbon Shenzhou-19 Mai Dakon ’Yan Sama Jannati
Wike ya bayyana hakan ne a yayin kaddamar da gina harsashin ginin kwalejin yaki da binciken sojoji da sauran hanyoyin da ke Ushafa a karamar hukumar Bwari da ke Abuja aranar Litinin.
Ya kuma ba da tabbacin cewa kowace karamar hukumar da ke Abuja za ta ci gajiyar ababen more rayuwa a cikin ajandar sabunta fata na gwamnati mai ci.
Ya ce, “A batun samar da ababen more rayuwa zuwa lokacin da wannan gwamnati ta kare a 2027, Abuja za ta zama wani abu daban.
“Ina mai tabbatar muku da cewa kowace karamar hukuma za a dauke ta da matukar muhimmanci. Ba ku bukatar nuna wani damuwa. Ajandar sabunta fata gaskiya ne. Ka ga ana cika duk wani alkawarin da aka dauka”.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp