• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani labarin kuma, Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta nesanta kanta daga goyon bayan Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

Mista Saidu, shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Najeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a takarar shugabancin majalisar dattawa zai haifar da halaka ga Arewacin Najeriya.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Samfurin Tianzhou-6
  • Yadda Hadin Gwiwa A Fannin Kiwon Lafiya Ke Amfanar Da Al’ummar Rwanda

Mamba a kungiyar ACF, Musa Saidu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Mista Saidu wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Nijeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a matsayin shugabancin majalisar dattawa zai durkusar da Arewacin Nijeriya.

“Don haka muna nesanta kanmu daga amincewa da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

“Gamayyar kungiyoyin ba sun yi magana ba ne da yawun ‘yan Arewa, sun yi magana ne bisa radin kansu.

 “Ba wata kungiyar Arewa ta gaskiya da za ta so amincewa da Akpabio a kan wani muhimmin matsayi irin na shugaban majalisar dattawa, saboda ba shi da alaka da Arewa.

“Mu ne mutanen da suka san Akpabio saboda mu mazauna Kudu ne, mun san wadanda ke son mutanen Arewa kuma Akpabio ba ya cikin su,” in ji shi.

Saidu ya kara da cewa tabbas gamayyar kungiyoyin sun amince da hakan ne bisa jahilci.

“Ina so in yi Allah wadai da amincewar da gamayyar kungiyoyin suka yi wa Akpabio, saboda sun yi hakan ne a kan jahilci.

“Zai iya yiyuwa an bai wa kungiyoyin cin hanci har tasa suka yi kwarin gwiwar amincewa da Akpabio.

“Ina tabbatar da cewa ‘yan Arewa ba mabarata ba ne da za su goyi bayan mutanen da ba su son su,” in ji shi.

Saidu ya ce ACF za ta ci gaba da yaki ko yin magana kan rashin adalci a kasar nan.

“Me ya sa jam’iyyar APC za ta himmatu wajen mayar da kujerar shugabancin majalisar dattawa ta 10 zuwa Kudu alhali muna da mutanen da suka cancanta a Arewa.

“Arewa maso yamma sun bai wa APC kuri’u mafi yawa a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, to me zai sa a hana su a dauka a bai wa wata shiyyar.

“Ina ganin lokaci ya yi da jam’iyyar za ta bai wa shiyyar ladan kuri’u masu yawa da ta bayar maimakon fara neman wani daga Kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa,” in ji shi.

Gamayyar kungiyoyin Arewa sun amince da Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa, inda suka ce shi ya fi dacewa da wannan mukamin.

Baya ga Mista Akpabio, tsohon gwamnan Jihar Abiya, Orji Uzor Kalu da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari duk sun bayyana sha’awarsu ta zama shugaban majalisar dattawa ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ACFGodswill AkpabioGoyon Baya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Kalubalanci G7 Da Ta Daina Taimakawa Wajen Matsa Lamba A Fannin Tattalin Arziki

Next Post

Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

Related

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

5 days ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

2 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
ACF
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

1 month ago
Next Post
Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.