ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
ACF

A wani labarin kuma, Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta nesanta kanta daga goyon bayan Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

Mista Saidu, shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Najeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a takarar shugabancin majalisar dattawa zai haifar da halaka ga Arewacin Najeriya.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Samfurin Tianzhou-6
  • Yadda Hadin Gwiwa A Fannin Kiwon Lafiya Ke Amfanar Da Al’ummar Rwanda

Mamba a kungiyar ACF, Musa Saidu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

ADVERTISEMENT

Mista Saidu wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Nijeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a matsayin shugabancin majalisar dattawa zai durkusar da Arewacin Nijeriya.

“Don haka muna nesanta kanmu daga amincewa da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

“Gamayyar kungiyoyin ba sun yi magana ba ne da yawun ‘yan Arewa, sun yi magana ne bisa radin kansu.

 “Ba wata kungiyar Arewa ta gaskiya da za ta so amincewa da Akpabio a kan wani muhimmin matsayi irin na shugaban majalisar dattawa, saboda ba shi da alaka da Arewa.

“Mu ne mutanen da suka san Akpabio saboda mu mazauna Kudu ne, mun san wadanda ke son mutanen Arewa kuma Akpabio ba ya cikin su,” in ji shi.

Saidu ya kara da cewa tabbas gamayyar kungiyoyin sun amince da hakan ne bisa jahilci.

“Ina so in yi Allah wadai da amincewar da gamayyar kungiyoyin suka yi wa Akpabio, saboda sun yi hakan ne a kan jahilci.

“Zai iya yiyuwa an bai wa kungiyoyin cin hanci har tasa suka yi kwarin gwiwar amincewa da Akpabio.

“Ina tabbatar da cewa ‘yan Arewa ba mabarata ba ne da za su goyi bayan mutanen da ba su son su,” in ji shi.

Saidu ya ce ACF za ta ci gaba da yaki ko yin magana kan rashin adalci a kasar nan.

“Me ya sa jam’iyyar APC za ta himmatu wajen mayar da kujerar shugabancin majalisar dattawa ta 10 zuwa Kudu alhali muna da mutanen da suka cancanta a Arewa.

“Arewa maso yamma sun bai wa APC kuri’u mafi yawa a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, to me zai sa a hana su a dauka a bai wa wata shiyyar.

“Ina ganin lokaci ya yi da jam’iyyar za ta bai wa shiyyar ladan kuri’u masu yawa da ta bayar maimakon fara neman wani daga Kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa,” in ji shi.

Gamayyar kungiyoyin Arewa sun amince da Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa, inda suka ce shi ya fi dacewa da wannan mukamin.

Baya ga Mista Akpabio, tsohon gwamnan Jihar Abiya, Orji Uzor Kalu da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari duk sun bayyana sha’awarsu ta zama shugaban majalisar dattawa ta 10.

ACF
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.