ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
ACF

A wani labarin kuma, Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta nesanta kanta daga goyon bayan Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

Mista Saidu, shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Najeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a takarar shugabancin majalisar dattawa zai haifar da halaka ga Arewacin Najeriya.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Samfurin Tianzhou-6
  • Yadda Hadin Gwiwa A Fannin Kiwon Lafiya Ke Amfanar Da Al’ummar Rwanda

Mamba a kungiyar ACF, Musa Saidu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

ADVERTISEMENT

Mista Saidu wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Nijeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a matsayin shugabancin majalisar dattawa zai durkusar da Arewacin Nijeriya.

“Don haka muna nesanta kanmu daga amincewa da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

LABARAI MASU NASABA

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

“Gamayyar kungiyoyin ba sun yi magana ba ne da yawun ‘yan Arewa, sun yi magana ne bisa radin kansu.

 “Ba wata kungiyar Arewa ta gaskiya da za ta so amincewa da Akpabio a kan wani muhimmin matsayi irin na shugaban majalisar dattawa, saboda ba shi da alaka da Arewa.

“Mu ne mutanen da suka san Akpabio saboda mu mazauna Kudu ne, mun san wadanda ke son mutanen Arewa kuma Akpabio ba ya cikin su,” in ji shi.

Saidu ya kara da cewa tabbas gamayyar kungiyoyin sun amince da hakan ne bisa jahilci.

“Ina so in yi Allah wadai da amincewar da gamayyar kungiyoyin suka yi wa Akpabio, saboda sun yi hakan ne a kan jahilci.

“Zai iya yiyuwa an bai wa kungiyoyin cin hanci har tasa suka yi kwarin gwiwar amincewa da Akpabio.

“Ina tabbatar da cewa ‘yan Arewa ba mabarata ba ne da za su goyi bayan mutanen da ba su son su,” in ji shi.

Saidu ya ce ACF za ta ci gaba da yaki ko yin magana kan rashin adalci a kasar nan.

“Me ya sa jam’iyyar APC za ta himmatu wajen mayar da kujerar shugabancin majalisar dattawa ta 10 zuwa Kudu alhali muna da mutanen da suka cancanta a Arewa.

“Arewa maso yamma sun bai wa APC kuri’u mafi yawa a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, to me zai sa a hana su a dauka a bai wa wata shiyyar.

“Ina ganin lokaci ya yi da jam’iyyar za ta bai wa shiyyar ladan kuri’u masu yawa da ta bayar maimakon fara neman wani daga Kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa,” in ji shi.

Gamayyar kungiyoyin Arewa sun amince da Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa, inda suka ce shi ya fi dacewa da wannan mukamin.

Baya ga Mista Akpabio, tsohon gwamnan Jihar Abiya, Orji Uzor Kalu da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari duk sun bayyana sha’awarsu ta zama shugaban majalisar dattawa ta 10.

ACF
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki

MASU ALAKA

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu
Tambarin Dimokuradiyya

2027:Gwamnoni Na Fuskantar Turjiya Wajen Gwagwarmayar Kare Kujerunsu Da Kuma Samar Da Magadansu

June 5, 2026
ACF
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Next Post
Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Mai Taken “Tides And Voices” A Birnin Sanya Na Sin

June 6, 2026
Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya

June 6, 2026
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai A Yankin Arewa Maso Gabashin Sin Ya Zarce 3,000 A Bana

June 6, 2026
Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

June 6, 2026
Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

Kafar CMG Ta Kulla Yerjeniyoyin Hadin Gwiwa Da Hukumomin Kasar Laos

June 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.