ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
ACF

A wani labarin kuma, Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta nesanta kanta daga goyon bayan Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

Mista Saidu, shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Najeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a takarar shugabancin majalisar dattawa zai haifar da halaka ga Arewacin Najeriya.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Samfurin Tianzhou-6
  • Yadda Hadin Gwiwa A Fannin Kiwon Lafiya Ke Amfanar Da Al’ummar Rwanda

Mamba a kungiyar ACF, Musa Saidu ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

ADVERTISEMENT

Mista Saidu wanda kuma shi ne shugaban kungiyar Arewa mazauna Kudancin Nijeriya, ya ce amincewa da Mista Akpabio a matsayin shugabancin majalisar dattawa zai durkusar da Arewacin Nijeriya.

“Don haka muna nesanta kanmu daga amincewa da Sanata Godswill Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa da gamayyar kungiyoyin Arewa suka yi.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

“Gamayyar kungiyoyin ba sun yi magana ba ne da yawun ‘yan Arewa, sun yi magana ne bisa radin kansu.

 “Ba wata kungiyar Arewa ta gaskiya da za ta so amincewa da Akpabio a kan wani muhimmin matsayi irin na shugaban majalisar dattawa, saboda ba shi da alaka da Arewa.

“Mu ne mutanen da suka san Akpabio saboda mu mazauna Kudu ne, mun san wadanda ke son mutanen Arewa kuma Akpabio ba ya cikin su,” in ji shi.

Saidu ya kara da cewa tabbas gamayyar kungiyoyin sun amince da hakan ne bisa jahilci.

“Ina so in yi Allah wadai da amincewar da gamayyar kungiyoyin suka yi wa Akpabio, saboda sun yi hakan ne a kan jahilci.

“Zai iya yiyuwa an bai wa kungiyoyin cin hanci har tasa suka yi kwarin gwiwar amincewa da Akpabio.

“Ina tabbatar da cewa ‘yan Arewa ba mabarata ba ne da za su goyi bayan mutanen da ba su son su,” in ji shi.

Saidu ya ce ACF za ta ci gaba da yaki ko yin magana kan rashin adalci a kasar nan.

“Me ya sa jam’iyyar APC za ta himmatu wajen mayar da kujerar shugabancin majalisar dattawa ta 10 zuwa Kudu alhali muna da mutanen da suka cancanta a Arewa.

“Arewa maso yamma sun bai wa APC kuri’u mafi yawa a zaben shugaban kasa na ranar 25 ga watan Fabrairu, to me zai sa a hana su a dauka a bai wa wata shiyyar.

“Ina ganin lokaci ya yi da jam’iyyar za ta bai wa shiyyar ladan kuri’u masu yawa da ta bayar maimakon fara neman wani daga Kudu a matsayin shugaban majalisar dattawa,” in ji shi.

Gamayyar kungiyoyin Arewa sun amince da Akpabio a matsayin shugaban majalisar dattawa, inda suka ce shi ya fi dacewa da wannan mukamin.

Baya ga Mista Akpabio, tsohon gwamnan Jihar Abiya, Orji Uzor Kalu da tsohon gwamnan Zamfara, Abdulaziz Yari duk sun bayyana sha’awarsu ta zama shugaban majalisar dattawa ta 10.

ACF
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

Ziyarar Shugaban Eritrea Za Ta Bunkasa Dangantakar Kasarsa Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.