• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
AFCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka tsara, a yau 13 ga watan Janairu aka fara gasar cin kofin Afirka karo na 34, kuma za a kammala ranar 11 ga watan Fabrairu a kasar Ibory Coast, wadda itace mai masaukin baki.

Sai dai gasar ta wannan karon za ta samu bakuncin zakakuran ‘yan wasa da tauraruwarsu take haskawa a duniya kuma sun buga wasanni a gasar a shekarun baya kuma har yanzu suna haskawa.

 

Muhammad Salah (Masar)

Masar ta yi rashin nasarar lashe kofin a hannun Senegal a shekara ta 2022 a Kamaru, sannan Senegal din ta hana Masar zuwa gasar Kofin Duniya da aka yi a kasar Katar a 2022. Dukkan wasannin a bugun fenariti Senegal ta yi nasara – kuma Salah bai buga fenaritin ba a AFCON, wanda shi ne na karshen bugawa, kuma kafin nan Senegal ta lashe kofin saboda ‘yan Masar ba su ci da yawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Kofin AFCON na bakwai da Masar ta dauka shi ne a shekarar 2010, kuma Salah na fatan taka rawar gani fiye da wadda ya yi a Gabon a 2017 da kuma a Kamru a shekarar 2022.

Salah ya dauki kofuna da yawa a Liberpool, sai dai zai so ya kara cin kwallo bayan shidan da ya zura a raga daga AFCON ukun da ya halarta, sannan yana son ya jagoranci Masar ta lashe gasar.

Kamar yadda yake taka rawar gani a Liberpool, a bana, Salah ne zai ja ragamar kasar a fafatawa da Ghana da Cape Berde da Mozambikue a rukuni na biyu.

 

Victor Osimhen (Nijeriya)

Dan wasa Bictor Osimhen ne ya lashe gwarzon dan kwallon Afirka na 2023 a bikin da aka yi ranar 11 ga watan Disamba sannan ya zama na farko da ya lashe kyautar daga Nijeriya tun bayan shekara ta 1999.

A shekara 2021 bai samu zuwa gasar ba sakamakon bullar cutar korona da raunin da ya ji, sai dai shin ko wanda ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afirka na bana zai ja ragamar Super Eagles ta lashe kofin na 2024?

Osimhen mai shekara 24 ya zama daya daga fitattun masu cin kwallaye a Turai, wanda ya zama kan gaba a cin kwallaye a SerieA, kuma hakan ya sa Napoli ta lashe kofin a karon farko tun bayan 1990.

Jinya da Osimhen ya yi ya sa Super Eagles ta yi canjaras da Lesotho da kuma Zimbabwe a wasan shiga gasar Kofin Duniya da za a yi a 2026, sannan tsohon dan wasan Lille din yana cikin tawagar Super Eagles a AFCON 2019, amma daga baya aka saka shi a wasan da kasar ta zama ta uku a wasannin.

Nijeriya tana rukunin da ya hada da mai masaukin baki Ibory Coast da Ekuatorial Guinea da Guinea-Bissau a rukunin farko.

 

Serhou Guirassy (Guinea)

Dan wasan na taka rawar gani a kungiyar kwallon kafa ta Stuttgard ta kasar Jamus, wanda ya ci kwallo 15 a wasanni 10 a gasar Bundesliga kuma dan wasan mai shekara 27, tsohon matashin tawagar Faransa zai buga AFCON a karon farko, bayan da ya fara yi wa Guine wasa a Maris din shekara ta 2022.

Rukuni na uku za a yi wasannin hamayya da ya kunshi mai rike da kofin Senegal da Kamaru, inda Syli National ke ciki da Gambia, wadda karo na biyu kenan da za ta kara a wasannin.

Raunin da ya ji a watan Nuwamba ya kawo masa tsaiko, amma dai Guinea na fatan Guirassy zai sa kwazon da zai kai kasar zagaye na biyu, inda daga nan komai zai iya faruwa.

 

Mohammed Kudus (Ghana)

Dan wasa Mohammed Kudus ya ci kwallo biyu lokacin da Ghana ta doke South Korea a gasar Kofin Duniya ta 2022 a Katar kuma Ghana za ta ziyarci makwabciyarta Ibory Coast da fatan ba za ta maimaita abin kunya da ta yi a Kamaru ba, inda aka fitar da ita a wasannin rukuni – har da wanda Comoros ta doke ta 3-2.

Ghana tana tangal-tangal a wasa biyu da ta buga a neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2026, wadda ta kara rashin nasara a hannun Comoros, sannan Kudus ne kan gaba a cin kwallaye da kasar ta samu gurbin zuwa Ibory Coast mai uku a raga, kuma yana taimaka wa West Ham United a wasan da take bugawa tun bayan da ya koma kungiyar da ke buga Premier League a cikin watan Agusta daga Ajad ta Holland.

Bayan da ya ci kwallo biyu a kofin duniya a Katar a 2022, ko dan wasan mai shekara 23 zai ja ragamar kasar ta taka rawar gani a Ibory Coast?

 

Azzedine Ounahi (Morocco)

Dan wasa Azzedine Ounahi yayi kokari sosai kuma rawar da dan wasan ya taka a gasar kofin duniya a Katar a 2022 a tawagar Morocco da ta kafa tarihin kai wa dab da karshe ta farko a Afirka – hakan ya sa Marseille ta dauki Ounahi.

Sai dai ya sha jinya tun raunin da ya ji a lokacin da yake buga wa tawagar Morocco wasa a watan Maris, bayan wasa bakwai da ya buga wa sabuwar kungiyarsa ta kasar Faransa.

Ounahi mai shekara 23 na aiki tukuru domin ya taka rawar gani a AFCON, koma ya yi fiye da kwazon da ya saka a gasar Kofin Duniya – sai dai dan wasan bai yi wa Morocco karawa biyu a neman shiga Kofin Duniya ba da ta yi a cikin Nuwamba. Kociyan tawagar, Walid Regragui zai so yin amfani da dan wasan da ya bayar da gudunmuwar da suka kai dab da karshe a kofin duniya, yayin da Morocco ke rukuni na shida da ya hada da Jamhurirae Congo da Zambia da kuma Tanzania.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AFCON 2023Cote d'IvoireOsimhen
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

Next Post

AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin ‘Yan Wasansa Na Yau

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

20 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

4 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

5 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

5 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

6 days ago
Next Post
AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin ‘Yan Wasansa Na Yau

AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin 'Yan Wasansa Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Kofin afirka

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.