• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
AFCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda aka tsara, a yau 13 ga watan Janairu aka fara gasar cin kofin Afirka karo na 34, kuma za a kammala ranar 11 ga watan Fabrairu a kasar Ibory Coast, wadda itace mai masaukin baki.

Sai dai gasar ta wannan karon za ta samu bakuncin zakakuran ‘yan wasa da tauraruwarsu take haskawa a duniya kuma sun buga wasanni a gasar a shekarun baya kuma har yanzu suna haskawa.

 

Muhammad Salah (Masar)

Masar ta yi rashin nasarar lashe kofin a hannun Senegal a shekara ta 2022 a Kamaru, sannan Senegal din ta hana Masar zuwa gasar Kofin Duniya da aka yi a kasar Katar a 2022. Dukkan wasannin a bugun fenariti Senegal ta yi nasara – kuma Salah bai buga fenaritin ba a AFCON, wanda shi ne na karshen bugawa, kuma kafin nan Senegal ta lashe kofin saboda ‘yan Masar ba su ci da yawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Kofin AFCON na bakwai da Masar ta dauka shi ne a shekarar 2010, kuma Salah na fatan taka rawar gani fiye da wadda ya yi a Gabon a 2017 da kuma a Kamru a shekarar 2022.

Salah ya dauki kofuna da yawa a Liberpool, sai dai zai so ya kara cin kwallo bayan shidan da ya zura a raga daga AFCON ukun da ya halarta, sannan yana son ya jagoranci Masar ta lashe gasar.

Kamar yadda yake taka rawar gani a Liberpool, a bana, Salah ne zai ja ragamar kasar a fafatawa da Ghana da Cape Berde da Mozambikue a rukuni na biyu.

 

Victor Osimhen (Nijeriya)

Dan wasa Bictor Osimhen ne ya lashe gwarzon dan kwallon Afirka na 2023 a bikin da aka yi ranar 11 ga watan Disamba sannan ya zama na farko da ya lashe kyautar daga Nijeriya tun bayan shekara ta 1999.

A shekara 2021 bai samu zuwa gasar ba sakamakon bullar cutar korona da raunin da ya ji, sai dai shin ko wanda ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afirka na bana zai ja ragamar Super Eagles ta lashe kofin na 2024?

Osimhen mai shekara 24 ya zama daya daga fitattun masu cin kwallaye a Turai, wanda ya zama kan gaba a cin kwallaye a SerieA, kuma hakan ya sa Napoli ta lashe kofin a karon farko tun bayan 1990.

Jinya da Osimhen ya yi ya sa Super Eagles ta yi canjaras da Lesotho da kuma Zimbabwe a wasan shiga gasar Kofin Duniya da za a yi a 2026, sannan tsohon dan wasan Lille din yana cikin tawagar Super Eagles a AFCON 2019, amma daga baya aka saka shi a wasan da kasar ta zama ta uku a wasannin.

Nijeriya tana rukunin da ya hada da mai masaukin baki Ibory Coast da Ekuatorial Guinea da Guinea-Bissau a rukunin farko.

 

Serhou Guirassy (Guinea)

Dan wasan na taka rawar gani a kungiyar kwallon kafa ta Stuttgard ta kasar Jamus, wanda ya ci kwallo 15 a wasanni 10 a gasar Bundesliga kuma dan wasan mai shekara 27, tsohon matashin tawagar Faransa zai buga AFCON a karon farko, bayan da ya fara yi wa Guine wasa a Maris din shekara ta 2022.

Rukuni na uku za a yi wasannin hamayya da ya kunshi mai rike da kofin Senegal da Kamaru, inda Syli National ke ciki da Gambia, wadda karo na biyu kenan da za ta kara a wasannin.

Raunin da ya ji a watan Nuwamba ya kawo masa tsaiko, amma dai Guinea na fatan Guirassy zai sa kwazon da zai kai kasar zagaye na biyu, inda daga nan komai zai iya faruwa.

 

Mohammed Kudus (Ghana)

Dan wasa Mohammed Kudus ya ci kwallo biyu lokacin da Ghana ta doke South Korea a gasar Kofin Duniya ta 2022 a Katar kuma Ghana za ta ziyarci makwabciyarta Ibory Coast da fatan ba za ta maimaita abin kunya da ta yi a Kamaru ba, inda aka fitar da ita a wasannin rukuni – har da wanda Comoros ta doke ta 3-2.

Ghana tana tangal-tangal a wasa biyu da ta buga a neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2026, wadda ta kara rashin nasara a hannun Comoros, sannan Kudus ne kan gaba a cin kwallaye da kasar ta samu gurbin zuwa Ibory Coast mai uku a raga, kuma yana taimaka wa West Ham United a wasan da take bugawa tun bayan da ya koma kungiyar da ke buga Premier League a cikin watan Agusta daga Ajad ta Holland.

Bayan da ya ci kwallo biyu a kofin duniya a Katar a 2022, ko dan wasan mai shekara 23 zai ja ragamar kasar ta taka rawar gani a Ibory Coast?

 

Azzedine Ounahi (Morocco)

Dan wasa Azzedine Ounahi yayi kokari sosai kuma rawar da dan wasan ya taka a gasar kofin duniya a Katar a 2022 a tawagar Morocco da ta kafa tarihin kai wa dab da karshe ta farko a Afirka – hakan ya sa Marseille ta dauki Ounahi.

Sai dai ya sha jinya tun raunin da ya ji a lokacin da yake buga wa tawagar Morocco wasa a watan Maris, bayan wasa bakwai da ya buga wa sabuwar kungiyarsa ta kasar Faransa.

Ounahi mai shekara 23 na aiki tukuru domin ya taka rawar gani a AFCON, koma ya yi fiye da kwazon da ya saka a gasar Kofin Duniya – sai dai dan wasan bai yi wa Morocco karawa biyu a neman shiga Kofin Duniya ba da ta yi a cikin Nuwamba. Kociyan tawagar, Walid Regragui zai so yin amfani da dan wasan da ya bayar da gudunmuwar da suka kai dab da karshe a kofin duniya, yayin da Morocco ke rukuni na shida da ya hada da Jamhurirae Congo da Zambia da kuma Tanzania.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AFCON 2023Cote d'IvoireOsimhen
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Suka Kamata A Sani Kan Noman Gyada

Next Post

AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin ‘Yan Wasansa Na Yau

Related

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or
Wasanni

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

12 hours ago
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
Wasanni

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

15 hours ago
Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya
Wasanni

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

17 hours ago
Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya
Wasanni

Lamine Yamal Zai Shafe Mako 3 Yana Jinya

2 days ago
PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai
Wasanni

PSG Ta Doke Barcelona Har Gida A Gasar Zakarun Turai

3 days ago
Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 
Wasanni

Mbappe Ya Jefa Kwallonsa Ta 60 A Gasar Zakarun Turai A Wasan Da Real Madrid Ta Doke Kairat 

4 days ago
Next Post
AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin ‘Yan Wasansa Na Yau

AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin 'Yan Wasansa Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.