• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki

by yahuzajere
2 years ago
zamfara

A yau Talata, Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki mai membobi 60, inda ya ƙara jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Zamfara.

Kwamitin mai membobi 60 a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar, an kaddamar da shi ne a Gusau, babban birnin jihar.

Sanarwar manema labarai da ofishin zababben gwamnan ya fitar dauke da rattaba hannun, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi ne gudanar da shirye-shiryen da suka dace domin karɓar mulki cikin kwanciyar hankali a jihar Zamfara.

Ya bayyana kwamitin mai membobi 60 a matsayin taron ƙwararru da ke da gogewar shekaru a ɓangarori daban-daban, waɗanda aka zaɓo su cikin tsanaki domin shiga cikin tsarin karɓar mulkin.

  • Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

“Canjin da al’ummar Zamfara suka zaɓa, canji ne daga rashin tsaro, rayuwar talauci, zuwa rayuwa ta tsaro, wadata da walwala, riƙon amana, da mutunta doka.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

“Kwamitin amsar mulkin mai membobi 60 an kafa shi ne da nufin fara dukkanin shirye-shiryen da ya kamata tare da kuma tsara yadda za a samu sauyi cikin sauƙi na sabuwar gwamnatinmu a jihar wanda zai fara aiki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

“An ɗorawa kwamitin alhakin samar da ingantaccen tsarin haɗin gwiwa da samar da hanyar sadarwa ta yau da kullum da Gwamnati mai barin gado tare da kuma karɓar ragamar gudanarwar gwamnati mai zuwa domin samun nasarar karɓar mulkin.

“Kwamitin zai kuma haɗa hannu da ma’aikatu, rassa da kuma hukumomi, sannan zai duba kuɗaɗen gwamnati mai barin gado tare da mai da hankali kan rasiɗai, ƙadarori, da kuma lamuni da sauransu.

“Al’ummar jihar Zamfara na da kyakkyawan fata; sun zaɓe mu ne cike da imanin za mu iya ceto tare da sake gina jiharmu.

“Mun kuma zaɓe ku a matsayin membobin kwamitin karɓar mulki saboda mun yi imanin cewa tsawon shekarun gogewarku da ƙwarewar ku, za mu iya aza harsashi ga gwamnati mai jiran gado domin ta yi nasara kan aikin ceton da ta sa gaba.

“Da wannan taƙaitaccen bayani da kuma yardar Allah, a halin yanzu, nake ƙaddamar da wannan kwamitin na karɓar mulki.”

A ranar 29 ga Mayun 2023 ne ake sa ran rantsar da sabon zababben gwamnan a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe
Labarai

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Next Post
Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

LABARAI MASU NASABA

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

An Shirya Harba Kumbon Shenzhou-21 A Kwanan Nan

October 24, 2025
Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

Shugaba Xi Ya Jagoranci Zaman Jin Ra’ayoyin Wadanda Ba ‘Yan JKS Ba Game Da Tsara Shirin Raya Kasa Karo Na 15 

October 24, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Naɗa Yayansa A Matsayin Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.