• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Aikin Ceto Muka Zo Yi, Inji Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara Yayin Ƙaddamar Da Kwamitin Karbar Mulki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata, Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da kwamitin karɓar mulki mai membobi 60, inda ya ƙara jaddada cewa ya zo aikin ceto ne tare da sake gina Zamfara.

Kwamitin mai membobi 60 a ƙarƙashin jagorancin tsohon Sufeto Janar na ‘yan sanda, M.D Abubakar, an kaddamar da shi ne a Gusau, babban birnin jihar.

Sanarwar manema labarai da ofishin zababben gwamnan ya fitar dauke da rattaba hannun, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, da yake jawabi a wajen ƙaddamar da kwamitin, Dauda Lawal, ya ce nauyin da ya rataya a kan kwamitin shi ne gudanar da shirye-shiryen da suka dace domin karɓar mulki cikin kwanciyar hankali a jihar Zamfara.

Ya bayyana kwamitin mai membobi 60 a matsayin taron ƙwararru da ke da gogewar shekaru a ɓangarori daban-daban, waɗanda aka zaɓo su cikin tsanaki domin shiga cikin tsarin karɓar mulkin.

  • Ina Da Yakinin Samun Nasara A Kotu -Dan Takarar Gwamnan APC A Bauchi

“Canjin da al’ummar Zamfara suka zaɓa, canji ne daga rashin tsaro, rayuwar talauci, zuwa rayuwa ta tsaro, wadata da walwala, riƙon amana, da mutunta doka.

Labarai Masu Nasaba

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

“Kwamitin amsar mulkin mai membobi 60 an kafa shi ne da nufin fara dukkanin shirye-shiryen da ya kamata tare da kuma tsara yadda za a samu sauyi cikin sauƙi na sabuwar gwamnatinmu a jihar wanda zai fara aiki a ranar 29 ga Mayu, 2023.

“An ɗorawa kwamitin alhakin samar da ingantaccen tsarin haɗin gwiwa da samar da hanyar sadarwa ta yau da kullum da Gwamnati mai barin gado tare da kuma karɓar ragamar gudanarwar gwamnati mai zuwa domin samun nasarar karɓar mulkin.

“Kwamitin zai kuma haɗa hannu da ma’aikatu, rassa da kuma hukumomi, sannan zai duba kuɗaɗen gwamnati mai barin gado tare da mai da hankali kan rasiɗai, ƙadarori, da kuma lamuni da sauransu.

“Al’ummar jihar Zamfara na da kyakkyawan fata; sun zaɓe mu ne cike da imanin za mu iya ceto tare da sake gina jiharmu.

“Mun kuma zaɓe ku a matsayin membobin kwamitin karɓar mulki saboda mun yi imanin cewa tsawon shekarun gogewarku da ƙwarewar ku, za mu iya aza harsashi ga gwamnati mai jiran gado domin ta yi nasara kan aikin ceton da ta sa gaba.

“Da wannan taƙaitaccen bayani da kuma yardar Allah, a halin yanzu, nake ƙaddamar da wannan kwamitin na karɓar mulki.”

A ranar 29 ga Mayun 2023 ne ake sa ran rantsar da sabon zababben gwamnan a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bagudu Ya Shiga Tsakani Kan Rikicin KAEDCO Da Sojoji

Next Post

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Tsaro

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

1 hour ago
Kotu
Tsaro

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

2 hours ago
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
Tsaro

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

3 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

5 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

16 hours ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

18 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

Sin Za Ta Karfafa Kare Namun Daji Karkashin Sabuwar Dokar Da Aka Kaddamar

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.