• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Hajjin 2024: Saudiyya Ta Karrama Jihar Sakkwato Da Babbar Lambar Yabo

by Abubakar Abba
1 year ago
in Labarai
0
Aikin Hajjin 2024: Saudiyya Ta Karrama Jihar Sakkwato Da Babbar Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mahukuntan kasar Saudiyya sun karrama gwamnatin Jihar Sakkwato da babbar lambar yabo bisa yadda gwamnatin jihar ta samu nasarar gudanar da ayyukan aikin hajji na 2024 da aka kammala.

Shugaban hukumar jin dadin alhazai Jihar Sakkwato, Aliyu Musa ne ya mika lambar yabon ga Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, a gidan gwamnatin jihar.

  • Shugaban Zanzibar Ta Tanzania: Ba Za Iya Raba Ci Gaban Afirka Da Sin Ba
  • DSS Ta Musanta Kai Samame Ofishin NLC Kan Zanga-zangar Yunwa

Musa ya shaida wa gwamnan cewa, Saudiyya ta karrama gwamnatin jihar da babbar lambar yabon ne saboda yadda tun da farko, gwamnatin jihar ta yi gagarumin shiri wajen kula jin dadi da walwalar alhazanta aikin hajjin bana da aka kammala.

A jawabinsa a lokacin da ya karbi babbar lambar yabon, Gwamna Aliyu, ya jinjina wa jami’an hukumar na jihar, bisa namijin kokarin da suka yi har ta kai ga gwamnatin jihar ta samun nasara a lokacin gudanar da aikin hajjin bana.

“Ina yi maku godiya bisa wannan namijin kokarin da kuka yi a lokacin gudanar da ayyukan hajjin bana, tabbas abin yabawa ne matuka.”

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A cewarsa, ciyar da alhazan jihar da gwamnatin jihar ta yi a Saudiyya a lokacin aikin hajjin bana, ba za a iya kwatantawa da na wasu jihohin ba, saboda haka, ku ci gaba da yin aiki mai kyau.

Kazalika, Aliyu ya bai wa hukumar tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa hukumar domin ta ci gaba da samun nansara a aikin hajji da ke tafe.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban hukumar ya gode wa gwamnan bisa bai wa hukumar dukkan wani goyon baya da ta bukata domin ta gudanar da aikin hajji a cikin nasara.

Shugaban ya kuma bai wa gwamnan tabbacin cewa shi da jami’ansa za su ci gaba da yin aiki tukuru, musamman domin su sauke nauyin da aka dora masu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Aikin Hajjin 2024KarramawaSakkwatoSaudiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lallai A Hukunta Waɗanda Suka Kai Mamaya Ofishin NLC – TUC

Next Post

Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari’a

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

23 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

9 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

10 hours ago
Next Post
Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari’a

Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari'a

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.