ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Aikin Hajjin 2024: Saudiyya Ta Karrama Jihar Sakkwato Da Babbar Lambar Yabo

by Abubakar Abba
2 years ago
Saudiyya

Mahukuntan kasar Saudiyya sun karrama gwamnatin Jihar Sakkwato da babbar lambar yabo bisa yadda gwamnatin jihar ta samu nasarar gudanar da ayyukan aikin hajji na 2024 da aka kammala.

Shugaban hukumar jin dadin alhazai Jihar Sakkwato, Aliyu Musa ne ya mika lambar yabon ga Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu, a gidan gwamnatin jihar.

  • Shugaban Zanzibar Ta Tanzania: Ba Za Iya Raba Ci Gaban Afirka Da Sin Ba
  • DSS Ta Musanta Kai Samame Ofishin NLC Kan Zanga-zangar Yunwa

Musa ya shaida wa gwamnan cewa, Saudiyya ta karrama gwamnatin jihar da babbar lambar yabon ne saboda yadda tun da farko, gwamnatin jihar ta yi gagarumin shiri wajen kula jin dadi da walwalar alhazanta aikin hajjin bana da aka kammala.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa a lokacin da ya karbi babbar lambar yabon, Gwamna Aliyu, ya jinjina wa jami’an hukumar na jihar, bisa namijin kokarin da suka yi har ta kai ga gwamnatin jihar ta samun nasara a lokacin gudanar da aikin hajjin bana.

“Ina yi maku godiya bisa wannan namijin kokarin da kuka yi a lokacin gudanar da ayyukan hajjin bana, tabbas abin yabawa ne matuka.”

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A cewarsa, ciyar da alhazan jihar da gwamnatin jihar ta yi a Saudiyya a lokacin aikin hajjin bana, ba za a iya kwatantawa da na wasu jihohin ba, saboda haka, ku ci gaba da yin aiki mai kyau.

Kazalika, Aliyu ya bai wa hukumar tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafa wa hukumar domin ta ci gaba da samun nansara a aikin hajji da ke tafe.

Tun da farko a jawabinsa, shugaban hukumar ya gode wa gwamnan bisa bai wa hukumar dukkan wani goyon baya da ta bukata domin ta gudanar da aikin hajji a cikin nasara.

Shugaban ya kuma bai wa gwamnan tabbacin cewa shi da jami’ansa za su ci gaba da yin aiki tukuru, musamman domin su sauke nauyin da aka dora masu.

Saudiyya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

MASU ALAKA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu
Labarai

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Next Post
Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari’a

Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari'a

LABARAI MASU NASABA

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.