• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Ministan Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa mai yuwuwa ta sake dawo wa gaban hadakar majalisar kasar don ta nemi amincewar ‘yan majalisar tarayya a kan kara yawan kasafin kudin 2024, amma idan ta samu kari kudaden shiga da ta ayyana za ta samu.

A makonnin da suka gabata ne, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa majalisar kudurin kasafin kudin 2024, wanda ya kai naira tirliyan 27.5.

  • Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

Ministan kudi da tattalin arziki, Mista Wale Edun shi ya bayyana hakan a lokacin da yake kare kasafin kudin a gaban kwamitin majalisa da ke kula da harkokin kudade.

Edun ya kuma shaida wa ‘yan kwamitin cewa, an samu gagarumin ci gaba a fannin tara kudaden shiga na kasar nan a ‘yan watan da suka gabata, inda ya kara da cewa, kudaden shigar na gwamnatin sun karu.
Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na yin dubi a kan yadda za ta kara hanzarta kashe kudin da ta ware a cikin kasafin kudin 2024.

A cewar Edun, kudin shigar ya kai kashi biyar a cikin dari, wanda hakan ya nuna wani kwarin gwiwa kan samun kudaden musaya duk da cewa darajar naira ya ragu, sannan akwai sauran bashin da ake bin gwamnatin wanda ya kai kimanin dala 46.

Labarai Masu Nasaba

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Ya kara da cewa bashin da gwamnatin ta biya ya kai kashi 18 a cikin dari, inda ya kai kasa da abin da aka ware a cikin kasafin kudin na badi.
Ministan ya sanar da cewa gibin da aka samu a kasafin kudin ana sa ran zai ragu daga naira tiriliyan 13.7 zuwa naira tirilyan 9.2.

Ya sanar da cewa, yawan kudin da za a amso bashi a cikin kasafin kudin ya ragu daga kashi 6.1 a cikin dari zuwa kashi 3.9.

Edu ya kara da cewa wannan kasafin kudi ne ta sake sabunta fata wannan kasa shi ya sa mai girma shugaban kasa ya aiwatar da shi cikin lokaci.

A nasa bangaren shugaban kwamtin harkokin kudade, Sanata Sani Musa ya bayyana cewa Nijeriya na cikin wani mawuyacin hali a fannin tattalin arziki, musamman a bangaren rashin aikin yi.

Sai dai, Musa ya ce yana da yakinin cewa, gwamnatin Shugaba Tinubu na kan yin dukkanin mai yuwa don lalubo da mafita a kan wannan kalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasafin Kudima'aikatar kudiMajalisar Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

Next Post

Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

Related

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

2 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

4 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

4 hours ago
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa
Labarai

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

5 hours ago
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

7 hours ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

10 hours ago
Next Post
Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.