• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Ministan Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa mai yuwuwa ta sake dawo wa gaban hadakar majalisar kasar don ta nemi amincewar ‘yan majalisar tarayya a kan kara yawan kasafin kudin 2024, amma idan ta samu kari kudaden shiga da ta ayyana za ta samu.

A makonnin da suka gabata ne, Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya gabatar wa majalisar kudurin kasafin kudin 2024, wanda ya kai naira tirliyan 27.5.

  • Kwamitin Majalisar Dattawa Ya Nemi A Karawa Ma’aikatar Yaɗa Labarai Kudi Kan Kasafin 2024
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

Ministan kudi da tattalin arziki, Mista Wale Edun shi ya bayyana hakan a lokacin da yake kare kasafin kudin a gaban kwamitin majalisa da ke kula da harkokin kudade.

Edun ya kuma shaida wa ‘yan kwamitin cewa, an samu gagarumin ci gaba a fannin tara kudaden shiga na kasar nan a ‘yan watan da suka gabata, inda ya kara da cewa, kudaden shigar na gwamnatin sun karu.
Ya ci gaba da cewa, gwamnatin na yin dubi a kan yadda za ta kara hanzarta kashe kudin da ta ware a cikin kasafin kudin 2024.

A cewar Edun, kudin shigar ya kai kashi biyar a cikin dari, wanda hakan ya nuna wani kwarin gwiwa kan samun kudaden musaya duk da cewa darajar naira ya ragu, sannan akwai sauran bashin da ake bin gwamnatin wanda ya kai kimanin dala 46.

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ya kara da cewa bashin da gwamnatin ta biya ya kai kashi 18 a cikin dari, inda ya kai kasa da abin da aka ware a cikin kasafin kudin na badi.
Ministan ya sanar da cewa gibin da aka samu a kasafin kudin ana sa ran zai ragu daga naira tiriliyan 13.7 zuwa naira tirilyan 9.2.

Ya sanar da cewa, yawan kudin da za a amso bashi a cikin kasafin kudin ya ragu daga kashi 6.1 a cikin dari zuwa kashi 3.9.

Edu ya kara da cewa wannan kasafin kudi ne ta sake sabunta fata wannan kasa shi ya sa mai girma shugaban kasa ya aiwatar da shi cikin lokaci.

A nasa bangaren shugaban kwamtin harkokin kudade, Sanata Sani Musa ya bayyana cewa Nijeriya na cikin wani mawuyacin hali a fannin tattalin arziki, musamman a bangaren rashin aikin yi.

Sai dai, Musa ya ce yana da yakinin cewa, gwamnatin Shugaba Tinubu na kan yin dukkanin mai yuwa don lalubo da mafita a kan wannan kalubalen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasafin Kudima'aikatar kudiMajalisar Tarayya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

Next Post

Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

Related

Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

2 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

3 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

6 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya
Ra'ayi Riga

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

9 hours ago
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas
Labarai

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

11 hours ago
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

13 hours ago
Next Post
Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

Kotun Ƙolin Nijeriya Ta Yi Watsi Da Buƙatar Sakin Nnamdi Kanu

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

An Kaddamar Da Gini Mara Fitar Da Hayakin Carbon Irinsa Na Farko A Duniya

August 24, 2025
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bita Na 3 Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasara A Yakin Kin Harin Japan

August 24, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

Ya Kamata A Kiyaye Sahihin Tarihi Da Rike Gaskiya

August 24, 2025
Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.