• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Akwai Yiwuwar Kara Mafi Karancin Albashi Zuwa Dubu 100 Ko 200 – NLC

by Sadiq
2 years ago
NLC

Kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta ce za a iya tattaunawa kan sabon mafi karancin albashi zuwa N100,000 ko N200,000 saboda tsadar rayuwa.

A yayin da kungiyar kwadago da kuma TUC suka shirya fara yajin aikin a ranar Talatar da ta gabata, sakamakon tasirin cire tallafin man fetur, sun ajiye yajin aikin ne bayan wata ganawar da suka yi da hukumomin gwamnati a Abuja da yammacin ranar Litinin.

  • ‘Yan Fashin Daji Sun Kashe Kansila A Katsina
  • Trump Ya Bayyana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Laifin Zamba

Sai dai a cewar shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero, sun dauki matakin ne domin bai wa gwamnati lokaci domin ta cika wani bangare na yarjejeniyar da aka cimma da kungiyoyin kwadago, inda ya kara da cewa bayar da karin albashin N35,000 – wani bangare na tayin gwamnati – ba sabon abu bane. mafi karancin albashin da ya ce a bai wa ma’aikata zai iya kai wa N200,000.

“Don haka, ba mafi karancin albashi ba ne abun dubawa. Don haka, idan a watan Maris, Afrilu, ko kafin lokacin za mu tattauna kan sabon albashi wanda zai iya zama N100,000 ko N200,000, za a rubuta shi a matsayin dokar mafi karancin albashi wanda ya kamata ya zama doka,” in ji shi a yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels.

Da yake tabbatar da cewa kyautar N35,000 ba kari ba ne a kan mafi karancin albashi na N30,000 na kasar, shugaban NLC ya ce za a yi la’akari da abubuwa da yawa game da sabon albashin.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

“Wasu abubuwa za su shigo cikin idan muka tattauna su- hauhawar farashin kayayyaki, tsadar rayuwa. Duk wani abu zai shigo ciki, ”in ji shi.

“Ba za mu je neman N65,000 ba.”

A cewarsa, domin sabon mafi karancin albashi ya fara aiki, majalisar dokokin kasar za ta taka muhimmiyar rawa.

“Mafi karancin albashi ya samo asali ne daga doka. Har sai an kafa shi a Majalisar Dokoki ta kasa, bai zana mafi karancin albashi ba,” Ajaero ya kara da cewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Ayyana Laraba A Matsayin Hutu Saboda Bikin Maulidi

Gwamnatin Kano Ta Ayyana Laraba A Matsayin Hutu Saboda Bikin Maulidi

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.