• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu Ya Gabatar Da Lacca Kan Fina-finan Nijeriya A Faransa

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ali nuhu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, Ali Nuhu ya gabatar da wata lacca a lokacin da ya halarci wani taro kan yadda fina-finan Nijeriya za su samu damar shiga kasashen duniya.

Taron wanda manyan masu ruwa da tsaki suka tabo batutuwa da sauran hanyoyin da za a bi wajen shigar da fina-finan Nijeriya lungu da sakon kasashen duniya.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

Manyan mutane daga Nijeriya da suka halarci wannan taro sun hada da tsohon ministan al’adu da yada labarai a lokacin mulkin shugaba, Muhammadu Buhari, Lai Muhammad, shugabar kwamitin bunkasa tattalin arzikin kasa ta hanyar fasaha da basirar zamani, Rahama Sadau da sauran manyan masu ruwa da tsaki a harkar fim a Nijeriya.

A wani rubutu da Ali Nuhu ya yi a shafinsa na sada zumunta na Facebook, an hango jarumin yana cewa, “Na gabatar da lacca a taron fina-finan Nijeriya na kasa da kasa a Cannes na kasar Faransa. Hankalina kacokan ya koma kan taken “Global Outreach for Nigerian Films: Opportunities and Limitations.”(Shigar Fina-finan Nijeriya zuwa kasashen duniya akwai damarmaki da kalubale).

“Na nuna karuwar sha’awar duniya game da labaru daban-daban, habakar ilimin zamani na dijital da muhimmancin hadin gwiwa tare da masu shirya fina-finai na duniya, wanda haka ne kadai zai zamto kamar wata hanya ta shigar da fina-finan da ake shiryawa daga kasashen duniya zuwa ko’ins cikin sauki.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

“Haka zalika, na tabo batun kalubalen da wannan yunkuri yake fuskanta da suka hada da karancin kudi, kayan aiki da kuma tallace-tallace da hanyoyin da za a bi wajen magance dukkan wadannan abubuwa a saukake.

“Ma’aikatar al’adu da kirkir-kirkire tana aiki tukuru don samar da tallafin kudi da kuma inganta hanyoyi da cibiyoyin kasuwanci kamar hada hannu dan manyan kamfanonin zuba jari irinsu ‘Afredimbank’ da sauransu wajen tallafa wa da dawo da martabar manyan masana’antun shirya fina-finai da suke neman durkushewa, inda muke fatan yin duk abin da ya dace kafin wani taron na NIFS da za a gudanar a wannan shekarar ta 2024 a Birnin Cannes.”

Ali Nuhu shi ne shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, wanda Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada a farko wannan shekarar ta 2024. Tun bayan nadin nasa jarumin yake nemo hanyoyin da wannan hukuma za ta bunkasa harkar shirya fina-finai a Nijeriya.

Inda zuwa yanzu ya halarci manyan taruka a ciki da wajen Nijeriya domin zakulo hanyoyin da masana’antun shirya fina-finai a Nijeriya za su yi gogayya da takwarorinsu na kasashen duniya ta hanyar kwarewa, ci gaba da kuma kayan aiki irin na zamani, wanda hakan zai sa su dinga shirya manyan fina-finan da za a yi alfahari da su har watakila su samu kyaututtuka kamar na Oscar da makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BollywoodHollywoodKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Next Post

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

3 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.