• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu Ya Gabatar Da Lacca Kan Fina-finan Nijeriya A Faransa

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ali nuhu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, Ali Nuhu ya gabatar da wata lacca a lokacin da ya halarci wani taro kan yadda fina-finan Nijeriya za su samu damar shiga kasashen duniya.

Taron wanda manyan masu ruwa da tsaki suka tabo batutuwa da sauran hanyoyin da za a bi wajen shigar da fina-finan Nijeriya lungu da sakon kasashen duniya.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

Manyan mutane daga Nijeriya da suka halarci wannan taro sun hada da tsohon ministan al’adu da yada labarai a lokacin mulkin shugaba, Muhammadu Buhari, Lai Muhammad, shugabar kwamitin bunkasa tattalin arzikin kasa ta hanyar fasaha da basirar zamani, Rahama Sadau da sauran manyan masu ruwa da tsaki a harkar fim a Nijeriya.

A wani rubutu da Ali Nuhu ya yi a shafinsa na sada zumunta na Facebook, an hango jarumin yana cewa, “Na gabatar da lacca a taron fina-finan Nijeriya na kasa da kasa a Cannes na kasar Faransa. Hankalina kacokan ya koma kan taken “Global Outreach for Nigerian Films: Opportunities and Limitations.”(Shigar Fina-finan Nijeriya zuwa kasashen duniya akwai damarmaki da kalubale).

“Na nuna karuwar sha’awar duniya game da labaru daban-daban, habakar ilimin zamani na dijital da muhimmancin hadin gwiwa tare da masu shirya fina-finai na duniya, wanda haka ne kadai zai zamto kamar wata hanya ta shigar da fina-finan da ake shiryawa daga kasashen duniya zuwa ko’ins cikin sauki.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

“Haka zalika, na tabo batun kalubalen da wannan yunkuri yake fuskanta da suka hada da karancin kudi, kayan aiki da kuma tallace-tallace da hanyoyin da za a bi wajen magance dukkan wadannan abubuwa a saukake.

“Ma’aikatar al’adu da kirkir-kirkire tana aiki tukuru don samar da tallafin kudi da kuma inganta hanyoyi da cibiyoyin kasuwanci kamar hada hannu dan manyan kamfanonin zuba jari irinsu ‘Afredimbank’ da sauransu wajen tallafa wa da dawo da martabar manyan masana’antun shirya fina-finai da suke neman durkushewa, inda muke fatan yin duk abin da ya dace kafin wani taron na NIFS da za a gudanar a wannan shekarar ta 2024 a Birnin Cannes.”

Ali Nuhu shi ne shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, wanda Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada a farko wannan shekarar ta 2024. Tun bayan nadin nasa jarumin yake nemo hanyoyin da wannan hukuma za ta bunkasa harkar shirya fina-finai a Nijeriya.

Inda zuwa yanzu ya halarci manyan taruka a ciki da wajen Nijeriya domin zakulo hanyoyin da masana’antun shirya fina-finai a Nijeriya za su yi gogayya da takwarorinsu na kasashen duniya ta hanyar kwarewa, ci gaba da kuma kayan aiki irin na zamani, wanda hakan zai sa su dinga shirya manyan fina-finan da za a yi alfahari da su har watakila su samu kyaututtuka kamar na Oscar da makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BollywoodHollywoodKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Next Post

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

3 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

LABARAI MASU NASABA

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.