• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ali Nuhu Ya Gabatar Da Lacca Kan Fina-finan Nijeriya A Faransa

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
Ali nuhu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, Ali Nuhu ya gabatar da wata lacca a lokacin da ya halarci wani taro kan yadda fina-finan Nijeriya za su samu damar shiga kasashen duniya.

Taron wanda manyan masu ruwa da tsaki suka tabo batutuwa da sauran hanyoyin da za a bi wajen shigar da fina-finan Nijeriya lungu da sakon kasashen duniya.

  • Gwamnatin Kebbi Ta Ayyana Asabar Ɗin Karshe Wata A Matsayin Ranar Tsaftar Muhalli
  • Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

Manyan mutane daga Nijeriya da suka halarci wannan taro sun hada da tsohon ministan al’adu da yada labarai a lokacin mulkin shugaba, Muhammadu Buhari, Lai Muhammad, shugabar kwamitin bunkasa tattalin arzikin kasa ta hanyar fasaha da basirar zamani, Rahama Sadau da sauran manyan masu ruwa da tsaki a harkar fim a Nijeriya.

A wani rubutu da Ali Nuhu ya yi a shafinsa na sada zumunta na Facebook, an hango jarumin yana cewa, “Na gabatar da lacca a taron fina-finan Nijeriya na kasa da kasa a Cannes na kasar Faransa. Hankalina kacokan ya koma kan taken “Global Outreach for Nigerian Films: Opportunities and Limitations.”(Shigar Fina-finan Nijeriya zuwa kasashen duniya akwai damarmaki da kalubale).

“Na nuna karuwar sha’awar duniya game da labaru daban-daban, habakar ilimin zamani na dijital da muhimmancin hadin gwiwa tare da masu shirya fina-finai na duniya, wanda haka ne kadai zai zamto kamar wata hanya ta shigar da fina-finan da ake shiryawa daga kasashen duniya zuwa ko’ins cikin sauki.

Labarai Masu Nasaba

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

“Haka zalika, na tabo batun kalubalen da wannan yunkuri yake fuskanta da suka hada da karancin kudi, kayan aiki da kuma tallace-tallace da hanyoyin da za a bi wajen magance dukkan wadannan abubuwa a saukake.

“Ma’aikatar al’adu da kirkir-kirkire tana aiki tukuru don samar da tallafin kudi da kuma inganta hanyoyi da cibiyoyin kasuwanci kamar hada hannu dan manyan kamfanonin zuba jari irinsu ‘Afredimbank’ da sauransu wajen tallafa wa da dawo da martabar manyan masana’antun shirya fina-finai da suke neman durkushewa, inda muke fatan yin duk abin da ya dace kafin wani taron na NIFS da za a gudanar a wannan shekarar ta 2024 a Birnin Cannes.”

Ali Nuhu shi ne shugaban hukumar Fina-finai ta Nijeriya, wanda Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya nada a farko wannan shekarar ta 2024. Tun bayan nadin nasa jarumin yake nemo hanyoyin da wannan hukuma za ta bunkasa harkar shirya fina-finai a Nijeriya.

Inda zuwa yanzu ya halarci manyan taruka a ciki da wajen Nijeriya domin zakulo hanyoyin da masana’antun shirya fina-finai a Nijeriya za su yi gogayya da takwarorinsu na kasashen duniya ta hanyar kwarewa, ci gaba da kuma kayan aiki irin na zamani, wanda hakan zai sa su dinga shirya manyan fina-finan da za a yi alfahari da su har watakila su samu kyaututtuka kamar na Oscar da makamantansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BollywoodHollywoodKannywood
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shen Yiqin Ta Jaddada Muhimmancin Tabbatar Da Kiwon Lafiya Da Walwalar Yara

Next Post

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Related

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

17 hours ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

7 days ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

1 week ago
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa
Nishadi

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

2 weeks ago
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

4 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

1 month ago
Next Post
Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

Tsarin Kiwon Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Kyautata, In Ji Jami’ar Hukumar Lafiyar Kasar

LABARAI MASU NASABA

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho

August 10, 2025
Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

Jihar Kogi Ta Kafa Kotuna 9 Don Hukunta Masu Cin Zarafin Mata

August 10, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

August 10, 2025
Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

August 10, 2025
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

August 10, 2025
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.