ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

by Sani Anwar
2 years ago
legas

Masu baje kolin kaya su kimanin 300, daga nahiyoyi biyar ne za su halarci bikin ciniki na kasa da kasa da ya shafi bangaren abinci da abin sha na Yammacin Afirka a wannan shekara, wanda ba a taba ganin irinsa ba.

Har ila yau, sama da masu baje koli 300 ne za su wakilci kasuwanci daban-daban daga sama da kasashe 50 a wannan baje koli da za a yi ranar 11 ga watan Yuni zuwa 13 na wannan shekara da muke ciki a Cibiyar Landmark da ke Jihar Legas, a Biktoriya Ailan.

  • Za A Yi Gaggarumin Taron Bunkasa Noma A Legas
  • Da Ɗumi-ɗumi: Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Jihar Legas, Soyannwo Ya Rasu Yana Da Shekara 55

Kasashe tara ne za su samu wuraren baje kolin kayansu, wadanda suka hada da Kasar Turkiyya, Dubai, Chana, Indiya, Amurka, Indonisiya, Itali, Egypt da kuma Tunisiya.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, manyan tawagogi daga Kasar Dubai, Ingila, Thailand, Ukraine, Ghana, Algeriya, Malesiya, Netherlands da kuma wasu kasashe da dama; za su yi amfani da wannan dama, don tallata sabbin kayayyakinsu a Nijeriya da Afirka ta Yamma tare kuma da haduwa da wasu sabbin abokan huldar kasuwanci.

Yanzu a wannan karo na biyar, Afirka ta Yamma a matsayinta na babbar yanki; ita ce za ta baje kolin abinci da abin sha a wajen wannan babban taro. Kazalika, ana sa ran baki akalla 6,000; za su halarci taro da za a dauki kwanaki uku ana aiwatar da shi.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Har wa yau, Manajan kula da baje kolin Brad Smith ya bayyana cewa, “baje kolin wannan shekara na kara nuni ne da samun karin yawan wadanda za su halarci wannan baje koli da kasashe da kuma karin kayayyaki fiye da kowane lokaci. Sannan, idan kuna neman sabbin kayayyaki masu ban sha’awa; wadanda har yanzu ba ku gani a kasuwannin Yammacin Afirka ba, ko shakka babu ba za a rasa a taron wannan baje koli ba.

“Baje kolin wannan shekara, ya karo yawan kasashen da za su baje kolin kayansu fiye da kowane irin lokaci a baya. Haka zalika, sabbin kayayyakinmu na Kasashen Amurka, Chana da kuma Itali, sunan shiga Kasashen Turkiyya, Dubai, Indiya, Indonisiya da kuma Egypt. Sannan kuma, muna maraba da masu baje koli a karon farko daga kasashe irin su Medico, Koreya, Hong Kong, Oman, Saudiyya, Algeriya, Iran, Libya, Turkmenistan da kuma Nepal”, in ji shi.

Kazalika, taron ya samu natija ne sakamakon yawan kasashen ketare da za su halarce shi, wanda ya yi matukar jan hankalin baki; musamman daga yankunan Afirka ta Yamma da sauran sassan duniya daban-daban.

“Don haka, muna yin alfahari da kanmu; a kan ingancin da muke da shi, wanda ya yi daidai da wanda ake bukata a duniya; wanda shi ne ya ba mu damar yin wannan wakilci.

Haka nan, wannan baje koli ne na musamman; wanda za mu kawo muku nau’ikan kamfanonin abinci da abubuwan sha na duniya zuwa wannan kasa Nijeriya tare da masu baje koli da masu ziyara da kuma dukkanin masu neman yin kasuwanci a yankunan Yammacin Afirka,” in ji Smith.

Daya daga cikin masu baje kolin kasa da kasa, rukunin kamfanin abinci na Dena; shi ne zai dauki nauyin wannan taro na Afirka ta Yamma. Wannan kamfani a Landan yake, sannan mai kamfanin wato, Dena babbar dila ce a bangaren sayar da kayan abinci, ta kuma kware tare da sanin sabbin abubuwan da ake amfani das u wajen sarrafa abincin, kama daga kan mai har zuwa sauran kayan hadi.

Har ila yau, wannan kamfani na ganin manyan damammaki a kasuwannin Nijeriya, lura da karuwar bukatar da ake samu a nan na samar da ingantattun kayayyaki.

“Bugu da kari, wannan baje koli da za a yi a wannan yanki na Afirka ta Yamma, zai yi matukar ba da dama; musamman wajen haduwar manyan kamfanonin abinci na wadannan yankuna na Yammacin Afirka,” in ji Kochhar, Shugaban Kasuwancin kasa da kasa.

“Mun yi imanin cewa, wannan abin aka kudiri niyyar yi; ya yi daidai da namu burin na fadada kasancewarmu a wajen da kuma kasashen da ke makwabtaka da mu. Wannan dalili ne, yasa muke kallon wannan taro a matsayin wani dandamali mai matukar muhimmanci; domin baje kolin abubuwan da muke da su.

“Manufarmu ta farko ita ce, kafa kungiyar abinci ta Dena a matsayin amintacce; sannan kuma wanda zai samar da abinci mai matukar inganci a kasuwannin Afirka.

Haka zalika, muna kuma da shirin kulla hadin gwiwa tare da manyan ‘yan kasuwa, Otel-otel da kuma gidajen sayar da abinci tare da baje kolin manyan nau’ikan kalolin kayayyakin abinci da suka hada da Filawa, Kwai, Man girki, Hatsi da sauran makamantansu.”

Wani daga cikin masu baje kolin na kasa da kasa, wato kamfanin Linc Drinks, shi ma daga Landan; wanda yake samar da lemukan shad a kuma barasa, Manajan wannan kamfani Zoryana Slater, ya yi matukar bayyana farincikinsa na kasancewa a wannan babban taro na baje koli.

“Burinmu shi ne, samar da dabarun hadin gwiwa da samar da hanyoyin baje kolin hajojinmu tare kuma da sanya wa mutane sha’awar kayayyakin da muke dauke das u, don su gani su kuma saya,” a cewar Zoryana Slater.

Legas
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.