ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Baje Kolin Kaya Kimanin 300 Za Su Halarci Bikin Kasuwancin Yammacin Afirka A Legas

by Sani Anwar
2 years ago
legas

Masu baje kolin kaya su kimanin 300, daga nahiyoyi biyar ne za su halarci bikin ciniki na kasa da kasa da ya shafi bangaren abinci da abin sha na Yammacin Afirka a wannan shekara, wanda ba a taba ganin irinsa ba.

Har ila yau, sama da masu baje koli 300 ne za su wakilci kasuwanci daban-daban daga sama da kasashe 50 a wannan baje koli da za a yi ranar 11 ga watan Yuni zuwa 13 na wannan shekara da muke ciki a Cibiyar Landmark da ke Jihar Legas, a Biktoriya Ailan.

  • Za A Yi Gaggarumin Taron Bunkasa Noma A Legas
  • Da Ɗumi-ɗumi: Mataimakin Shugaban Ma’aikatan Jihar Legas, Soyannwo Ya Rasu Yana Da Shekara 55

Kasashe tara ne za su samu wuraren baje kolin kayansu, wadanda suka hada da Kasar Turkiyya, Dubai, Chana, Indiya, Amurka, Indonisiya, Itali, Egypt da kuma Tunisiya.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, manyan tawagogi daga Kasar Dubai, Ingila, Thailand, Ukraine, Ghana, Algeriya, Malesiya, Netherlands da kuma wasu kasashe da dama; za su yi amfani da wannan dama, don tallata sabbin kayayyakinsu a Nijeriya da Afirka ta Yamma tare kuma da haduwa da wasu sabbin abokan huldar kasuwanci.

Yanzu a wannan karo na biyar, Afirka ta Yamma a matsayinta na babbar yanki; ita ce za ta baje kolin abinci da abin sha a wajen wannan babban taro. Kazalika, ana sa ran baki akalla 6,000; za su halarci taro da za a dauki kwanaki uku ana aiwatar da shi.

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Har wa yau, Manajan kula da baje kolin Brad Smith ya bayyana cewa, “baje kolin wannan shekara na kara nuni ne da samun karin yawan wadanda za su halarci wannan baje koli da kasashe da kuma karin kayayyaki fiye da kowane lokaci. Sannan, idan kuna neman sabbin kayayyaki masu ban sha’awa; wadanda har yanzu ba ku gani a kasuwannin Yammacin Afirka ba, ko shakka babu ba za a rasa a taron wannan baje koli ba.

“Baje kolin wannan shekara, ya karo yawan kasashen da za su baje kolin kayansu fiye da kowane irin lokaci a baya. Haka zalika, sabbin kayayyakinmu na Kasashen Amurka, Chana da kuma Itali, sunan shiga Kasashen Turkiyya, Dubai, Indiya, Indonisiya da kuma Egypt. Sannan kuma, muna maraba da masu baje koli a karon farko daga kasashe irin su Medico, Koreya, Hong Kong, Oman, Saudiyya, Algeriya, Iran, Libya, Turkmenistan da kuma Nepal”, in ji shi.

Kazalika, taron ya samu natija ne sakamakon yawan kasashen ketare da za su halarce shi, wanda ya yi matukar jan hankalin baki; musamman daga yankunan Afirka ta Yamma da sauran sassan duniya daban-daban.

“Don haka, muna yin alfahari da kanmu; a kan ingancin da muke da shi, wanda ya yi daidai da wanda ake bukata a duniya; wanda shi ne ya ba mu damar yin wannan wakilci.

Haka nan, wannan baje koli ne na musamman; wanda za mu kawo muku nau’ikan kamfanonin abinci da abubuwan sha na duniya zuwa wannan kasa Nijeriya tare da masu baje koli da masu ziyara da kuma dukkanin masu neman yin kasuwanci a yankunan Yammacin Afirka,” in ji Smith.

Daya daga cikin masu baje kolin kasa da kasa, rukunin kamfanin abinci na Dena; shi ne zai dauki nauyin wannan taro na Afirka ta Yamma. Wannan kamfani a Landan yake, sannan mai kamfanin wato, Dena babbar dila ce a bangaren sayar da kayan abinci, ta kuma kware tare da sanin sabbin abubuwan da ake amfani das u wajen sarrafa abincin, kama daga kan mai har zuwa sauran kayan hadi.

Har ila yau, wannan kamfani na ganin manyan damammaki a kasuwannin Nijeriya, lura da karuwar bukatar da ake samu a nan na samar da ingantattun kayayyaki.

“Bugu da kari, wannan baje koli da za a yi a wannan yanki na Afirka ta Yamma, zai yi matukar ba da dama; musamman wajen haduwar manyan kamfanonin abinci na wadannan yankuna na Yammacin Afirka,” in ji Kochhar, Shugaban Kasuwancin kasa da kasa.

“Mun yi imanin cewa, wannan abin aka kudiri niyyar yi; ya yi daidai da namu burin na fadada kasancewarmu a wajen da kuma kasashen da ke makwabtaka da mu. Wannan dalili ne, yasa muke kallon wannan taro a matsayin wani dandamali mai matukar muhimmanci; domin baje kolin abubuwan da muke da su.

“Manufarmu ta farko ita ce, kafa kungiyar abinci ta Dena a matsayin amintacce; sannan kuma wanda zai samar da abinci mai matukar inganci a kasuwannin Afirka.

Haka zalika, muna kuma da shirin kulla hadin gwiwa tare da manyan ‘yan kasuwa, Otel-otel da kuma gidajen sayar da abinci tare da baje kolin manyan nau’ikan kalolin kayayyakin abinci da suka hada da Filawa, Kwai, Man girki, Hatsi da sauran makamantansu.”

Wani daga cikin masu baje kolin na kasa da kasa, wato kamfanin Linc Drinks, shi ma daga Landan; wanda yake samar da lemukan shad a kuma barasa, Manajan wannan kamfani Zoryana Slater, ya yi matukar bayyana farincikinsa na kasancewa a wannan babban taro na baje koli.

“Burinmu shi ne, samar da dabarun hadin gwiwa da samar da hanyoyin baje kolin hajojinmu tare kuma da sanya wa mutane sha’awar kayayyakin da muke dauke das u, don su gani su kuma saya,” a cewar Zoryana Slater.

Legas
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

LABARAI MASU NASABA

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

Rahoton Bankin Duniya: Ci Gaban Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Dore

July 7, 2026
Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

Binciken CGTN Ya Shaida Kiraye-kirayen Jama’a Game Da Bukatar Hada Karfi Da Karfe Wajen Shawo Kan Kalubalen Tsanantar Yanayi

July 7, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Na ADC, Ya Gana da El-Rufai, Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Mulkin APC

July 7, 2026
Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

Kulla Yarjejeniyar UNCLOS Da Aiwatar Da Ita Jigo Ne Na Wanzar Da Gaskiya Da Adalci A Odar Teku Tsakanin Kasa Da Kasa

July 7, 2026
Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

July 7, 2026
Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

Gwajin Harba Makamai Masu Linzami Aiki Ne Na Horarwa Da Sojojin Kasar Sin Ke Gudanarwa

July 7, 2026
'yansanda

Yansanda Sun Kai Samame Maɓoyar Masu Laifi, Sun Kama Mutane 150 A Legas

July 7, 2026
Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.