• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Arewa: Bango Ne Ya Tsage Kadangare Ya Samu Wurin Shiga

by Sulaiman and Imam Murtadha Muhammad Gusau
9 months ago
in Bakon Marubuci
0
arewa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai. Assalamu alaikum. 

Ya ku ‘yan uwana masu daraja, masu albarka ‘yan Arewa! Ku sani, har gobe ruwa yana maganin dauda. Har gobe Arewa Arewa ce. Har gobe, ko da goma ta lalace tafi biyar albarka. Mu har gobe Arewar mu Arewarmu ce. Bamu da inda yafi ta duk duniya. Babu wani wuri da muke so da kuma kauna fiye da ita. Don haka, kar ku taba yarda a sare maku gwiwa. Kar ku taba yarda a bata maku ginshikin ku.

 

Duk yadda wasu ‘yan kudu za su soki Arewa, duk yadda zasu Bata ta, duk yadda za su kushe ta, duk yadda za su yi wasu maganganu na shirme, maganganu na cin mutunci, maganganu na batanci akan Arewa, wallahi babu wanda zai iya sa mu kalli Arewa da wani mummunan kallo. Su ma sun sani, Arewa ba kanwar lasa bace. Sun sani, ba’a iya yi sai da Arewa. Sun sani, dan Arewa yafi karfin raini da wulakanci.

 

Labarai Masu Nasaba

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

Waraka Daga Bashin Ketare

Idan kun lura da kyau, zaku ga wasu marasa kishi, ‘yan uwanmu ‘yan Arewa, suna ta famar ture-turen wasu rubuce-rubucen ‘yan kudu, wanda suka yi suka soki Arewa da ‘yan Arewa, akan wannan zanga-zanga da ta faru, wai suna kafa muna hujja da wadancan rubutuce- rubucen. To muna kira ga ‘yan Arewa, su yi watsi da wancan shirmen, suyi watsi da irin wannan hali na karantawa, da wadancan ‘yan uwan mu suka dauka.

 

Mu mun fi karfin a razana mu da rubutun wasu mutane. To ma wai yau ne suka fara rubuce-rubucen nasu na batanci akan Arewa da ‘yan Arewa, bare har rubutun su ya razana mu, ko ya bamu tsoro, ko ya tayar mana da hankali?

Don haka duk wasu rubuce-rubucen da za su yi, saboda kawai an yi zanga-zanga a Arewa, mu wannan kallon su muke yi a matsayin masu shirme, masu bata lokacin su a banza. Kuma ai ma sun samu masu goyon baya ne daga wasu ‘yan Arewar, na aci mutuncin Arewa da ‘yan Arewa, shi yasa suka samu damar yin wasu rubuce-rubucen banza da wofi, rubuce-rubucen iska da shirme, rubuce-rubuce marasa kan gado. Yo dama kai dan Arewa kana tsammanin su rubuta wani abin arziki a kan ka? To idan wannan shine tunaninka, ka sani ka makaro. Don haka, mu a tunanin mu, duk wani rubutu na batanci da ‘yan kudu za su yi akan Arewa, wannan ba sabon abu bane. Mu kawai bakin cikin mu, bai fi wadanda aka samu daga Arewar, suna goya masu baya ba.

 

Ai dan Arewa wallahi idan ba’a yaba masa ba a kasar nan, to kuwa ba za’a zage shi ko a hantare shi ba. Don girman Allah wane irin hakuri ne dan Arewa bai yi ba a kasar nan? Wane irin cin kashi ne ba’a yiwa ‘yan Arewa ba a mulkin kasar nan? Sannan shin ma wai don Allah a Arewa ne aka fara yin zanga-zanga a kasar mu Nijeriya?

 

Idan ana maganar daga tutar wata kasa, duk mai bibiyar ayyukan ‘yan kungiyar IPOB a Nijeriya, na yankin inyamurai, ya san da cewa babu ranar da IPOB ba za su daga turar kasar Isra’ila ba. Sannan domin Allah a cikin kasahen da suke taimakawa kabilar Inyamurai, suka yakki Nijeriya, a lokacin yakin basasa, babu kasar Isra’ila ne?

Sannan a lokacin da aka yi zanga-zangar ENDSARS a kasar nan, don Allah wace tuta suka daga? Kowa ya kalli irin yadda suke yawo ko’ina a garuruwansu, suna kaga tutar kasar Amerika. Amma don me yasa bamu ji an taba ayyana cewa wannan cin amanar kasa ba ne, wato sai yanzu da yazo akan Arewa da ‘yan Arewa ko? Kawai don an raina mu ne, don an raina mana wayo, an raina mana hankali, an dauke mu ba ‘yan kasa ba, an dauke mu marasa wayo.An dauke mu bakin-haure ko?

Don Allah wane irin kone-kone, da sace-sacen dukiya, da kashe-kashe, da fasa shaguna ne ba’a yi ba a zanga-zangar ENDSARS, lokacin mulkin Buhari? Amma daga karshe, ba manyan su bane da wasu kasashen duniya, suka daure masu gindi, suka ce an zalunce su, har kotu aka je, daga karshe aka sanya gwamnati ta biya wasu kudade ga wasu mutane da suka yi zanga-zangar ENDSARS?

Kuma wai har an samu wasu daga cikin mu, idon su ya rufe basu hango gaskiyar lamurra.

Mu ‘yan Arewa, babu ruwan mu da kabilanci, domin ba shi muka sa a gaba ba, amma mun ga rainin wayon yana neman yayi yawa ne, shi yasa kuka ga muna yin duk wadannan bayanan.

A yau, a kasar nan, muna gani kiri-kiri, shugaban kungiyar yarbawa zalla ta OPC, wato Ganiyu Adams, babu irin ta’addancin da bai yi ba a kasar nan. Babu irin barnar da basu yi ba, amma an wayi gari yau shi ne abin girmamawa ne a wurin mutanen sa. Sun tsaya masa, sun daure masa gindi, manyan yankinsa suna tare da shi, basa zagin sa, basa hantarar sa, basa wulakanta shi, basa ci masa mutunci, kai daga karshe ma har sarautar gargajiya suka bashi, ta sarautar ARE ONA KAKAMFO, sarautar da ba’a baiwa kowa ita, sai wanda yake jarumi, hamshaki, babban mutum a cikinsu. Kaje ka binciki tarihi da matsayin wannan sarautar da aka bashi.

Yau a yankin kasar Ibo, muna kallon irin yadda suka dauki Mazi Nnamdi Kanu, dan gwagwarmayar samun kasar Biyafara. Wallahi Nnamdi Kanu ya fi duk wani dan siyasa, ya fi duk wani mai kudi, ko mai sarauta, a yankin kasar Ibo baki daya, kuma ba don komai ba, kawai don yana gwagwarmayar neman ‘yanci masu ‘yanci, kamar yadda suke kallo. Don Allah, wace irin barna ce basu yi ba a kasar nan? Wane irin ta’addanci ne basu yi ba, da sunan kwatar ‘yanci? Amma an wayi gari, tun daga Sarakunansu, har zuwa ‘yan siyasar su, har zuwa masu arzikinsu, duk sun tsaya masa, akan su sam ma ba su yarda cewa shi mai laifi ba ne, kuma suna nan suna ta fadi-tashin ganin lallai sai gwamnati ta sake shi. Wannan kawai duk a takaice ke nan fa.

Sannan ina Sunday Igboho, dan gwagwarmayar tabbatar da kasar yarbawa zalla? Wane irin zagi da cin mutunci ne bai yiwa kasar nan ba? Wane irin zagi da cin mutunci ne bai yiwa kabilun Hausa-Fulani ba? Wane irin ta’addanci ne bai yi ba, da sunan kafa kasar kabilar yarbawa zalla? Amma an wayi gari, wannan mutum ya zama babban jarumi a cikin su, ya zama abin girmamawa. Ka tafi gidan sa, ka ga yadda ‘yan siyasar su, da Sarakunan su, da masu kudin su, kai da kowa na su, har da malaman addinin su, ka ga irin yadda suke kai masa ziyara, suna girmamawa shi. Sun dauke shi wani irin babban jarumi, suna bashi kariya, fiye da yadda kake zato. Har kama shi an yi, aka tsare shi, amma manyan su da ‘yan siyasar su, da Sarakunan su, da masu kudinsu, wallahi duk sun bayar da gudummawa wurin kubutar da shi.

Ka tafi yankin Neja Delta, ka ga yadda ‘yan gwagwarmayar kwatar ‘yancin su suka zama wasu irin hamshakai, abin girmamawa a cikin al’ummar su. Za ka ga irin girman da ake ba su ya fi na Sarakuna, yafi na masu arziki, da ‘yan siyasa. Sun yi kudi na fitar hankali, fiye da yadda ake zato.Wasu daga cikin su ma har kwangiloli masu tsoka ake basu daga gwamnati, irin su Tampolo, irin su Mujahid Asari Dokubo , da dai sauransu. Wasu ma duk an kai su kasashen waje sun yi karatu, sun koyi sana’oi kuma daga baya gwamnati ta basu aikin yi.

Wadannan fa duk na kwana-kwanan nan ne, ban da wadanda suka wuce a can da. Kuma wannan duk ina kawo maku sune a takaice.

Amma abin bakin ciki shine, da ka zo yankin mu na Arewa mai albarka, zaka tarar abin ba haka yake ba. Su su zage ku, wasu ‘yan uwanka ma ‘yan Arewar su zage ku. Abin ya zamarwa matasan Arewa da talakawansu da al’ummar Arewa baki daya, GABA KURA BAYA SIYAKI.

Matashin Arewa a yau, an wayi gari ya rasa inda zai sa kansa. Ya rasa mafita. Ya rasa wanda zai kama hannunsa yace masa, kai wannan daidai ne, wannan ba daidai ne ba.

Talakawan Arewa da matasanmu da al’ummarmu, an hana su noma da kiwo da sana’o’in da suka saba yi, sun rasa inda za su sa kawunan su, saboda mummunan rashin tsaro da yake addabar mu, kuma sun fito domin su nuna damuwar su akan hakan, saboda kawai an samu kuskure, saboda wasu miyagun mutane da aka yo haya, sun shiga, sun bata masu lamari, shine sai su zama abin zagi, abin cin mutunci da hantara? Sam ba zata sabu ba, wai bindiga a ruwa!

Eh, dukkanin mu mun yi ittifaki cewa, tashe-tashen hankula, kone-kone, kashe-kashe, da sace-sace, da fasa shaguna, da zubar da jinin bayin Allah duk abubuwa ne marasa kyawu, abubuwa ne da ba su dace ba, wadanda matasan mu, talakawa suka yi da sunan zanga-zanga.To amma don girman Allah, idan zamu yiwa kan mu adalci, sai mu tambayi kawunan mu, me ya jawo faruwar hakan? Shin da ace hukumomi sun kula da hakkin matasa da talakawa, yadda ya dace, da hakan ai bata faru ba ko?

Kuma ku duba ku gani fa, ‘yan Arewa a yanzu suna cikin tsaka mai wuya ne. Domin idan ba’a yi hankali ba, idan bamu yi hattara ba, yadda shekaru takwas din shugaba Buhari suka zamar wa ‘yan Arewa marasa amfani, yanzu ma fa haka muke hange a cikin wannan mulkin fa!

Kuma ya kamata mu kara sani, ba wani abu bane matsalar Arewa ba illa, rashin hadin kai, yi ma juna hassada, cin dunduniyar juna, rashin girmama fahimta da ra’ayin juna.Rashin son ci gaban juna, kokarin kwarewa juna baya, sannan babban laifin shine, hada kai da ake yi da wasu daga cikin ‘yan Arewar, domin aci amanarta da ta ‘ya’yanta.

Don haka, da yardar Allah, mu ba zamu gushe ba muna addu’a da rokon Allah Subhanahu wa Ta’ala, akan matsalolin da suke damun mu a kasar nan da kuma yankin Arewa. Zamu ci gaba da fadawa Allah yayi mana maganin duk wasu masu zaluntarmu a kasar nan!

Zamu ci gaba da addu’a da rokon Allah, duk wanda yake da hannu cikin kawo mana rashin tsaron a Arewa da Nijeriya baki daya, Allah yayi mana maganinsa. Duk wanda yake murkushe kudin da ake warewa domin samar da tsaro, yana sha’anin gabansa, Allah yayi mana maganinsa. Duk wanda yake hada baki da ‘yan ta’adda, ana sace mu, ana kashe mu, ana zubar da jinin mu, ana hana mu noma da kiwo da sana’o’i, Allah yayi mana maganinsa. Duk wani azzalumin dan kasuwa da yake da hannu wurin haifar da tashi da hauhawar farashin kayayyaki, babu gaira babu dalili, Allah yayi mana maganinsa. Duk wani shugaba a cikin wannan al’ummah, wanda baya tausayinmu, Allah yayi mana maganinsa. Duk wanda yake da hannu wurin kwashe kudin talakawa, yana jin dadi daga shi sai iyalansa, da duk masu taimaka masu, Allah yayi muna maganinsu. Duk wani azzalumi da yake kan mulki, da duk wani azzalumi da yake cikin daji, da na cikin gari, suna cutar da al’ummah, Allah yayi mana maganinsu. Allah ya isar mana, Allah ya saka mana ga duk wani mugu, azzalumi, amin Ya Hayyu Ya Kayyum, Ya Zal Jalali Wal-Ikram!

Allah ya sawwake, amin.

Dan uwanku, Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuta, daga Okene, Jihar Kogi


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazari Kan Samun Kudin Shiga Ta Hanyar Kiwon Kajin Gida

Next Post

Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

Related

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

4 weeks ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

1 month ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

2 months ago
Next Post
Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

Cututtukan Da Suka Fi Addabar Kajin Gidan Gona Lokacin Damina

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

Dakarun Soji Sun Daƙile Wani Sabon Harin ISWAP A Dikwa

May 14, 2025
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

May 14, 2025
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

May 14, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.