• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnan kano

A wani taron gaggawa da ‘yan kasuwan Jihar Kano, gwamnan Kabir Yusuf ya misalta cewa al’umman jihar na fama da matsatsin rayuwa da fatara mai muni.   

Ya shaida wa ‘yan kasuwan cewa, “Akwai fatara a Kano kuma dole ne mu nemo mafita domin tsaida mutuwar. Al’ummarmu da suke fadi su mutu ko su kamu da rashin lafiya. Mun sani kuna iya bakin kokarinku a matsayinku na ‘yan kasuwa, amma ba wai kuna yin iyaka abun da ya dace ku yi ba kenan.

  • Shugaban Karamar Hukuma A Kano Ya Yi Murabus, Wani Kuma Ya Fice Daga APC Zuwa NNPP
  • Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta

“Dole mu hada karfi da karfe waje guda mu nemo mafita, a matsayina na gwam-na da mataimakina ba mu bukatar komai daga wajen kowa. Kawai abun da muke da bukata shi ne ku zo ku taimaka mana domin mu taimaki talakawanmu.”

Gwamna Yusuf ya bukaci ‘yan kasuwan da su taimaka wa kokarin gwamnatin ji-har, ya ce, “Ina rokonku da ku nemi hanyoyin rage farashin kayan masarufi domin saukaka wa jama’a.

“Kano cibiyar kasuwanci ce a Nijeriya baya ga Legas. Jihar tana samun kama-baya kowacce rana.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

“A baya, ‘yan kasuwa su na zuwa daga jihohin makwafta da ma kasashen waje domin yin sayayya a Jihar Kano, amma wannan lamarin na fuskantar tangarda.

“Manyan ‘yan kasuwan daga Nijar, Kamaru, Chadi da wasu sun maida Kano kamar gidansu. Amma a yau dukkaninsu sun canza. Sayan kayanmu ya ragu.

“Akwai damarmakin ayyukan yi sosai a Jihar Kano kuma akwai kamfanoni da daman gaske wadanda suke taimaka wa rayuwar al’umman. Sai dai a yanzu wasu sun zama tarihi. Wannan matsalar ya sanya matasa sun shiga harkokin shaye-shaye, garkuwa da mutane da fashin daji. Mutane su na rayuwa cikin tsananin ta-lauci, yayin da wasu ko mudun shinkafa ba su iya saye domin iyalansu su ci.

“Zan nemi ganin Shugaban kasa Bola Tinubu na shaida masa irin yunwar da ke addabar al’ummar Kano. Dole gwamnatin tarayya ta bayar da muhimmin tallafi ga jihar da ke da mutane masu tarin yawa.”

Wasu da suka yi magana a madadin ‘yan kasuwan kamar Alhaji Sabiu Bako, Alhaji Salisu Sambajo, Muhammad Adakawa, da Sammani Elsamad, gami da saura sun yi kira ga gwamna Yusuf da ya jagoranci sauran gwamnonin shiyyar arewa maso yamma domin nemo hanyoyin shawo kan matsalolin tattalin arziki da ke addabar al’ummar shiyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Next Post
cmg

An Nuna Dandanon Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG A Filin Jiragen Sama Da Yankunan Kasuwanci Na Dubai

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara

October 16, 2025
Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.