• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Al’ummar Kano Na Mutuwa Da Yunwa Da Fatara – Gwamna Yusuf  

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnan kano

A wani taron gaggawa da ‘yan kasuwan Jihar Kano, gwamnan Kabir Yusuf ya misalta cewa al’umman jihar na fama da matsatsin rayuwa da fatara mai muni.   

Ya shaida wa ‘yan kasuwan cewa, “Akwai fatara a Kano kuma dole ne mu nemo mafita domin tsaida mutuwar. Al’ummarmu da suke fadi su mutu ko su kamu da rashin lafiya. Mun sani kuna iya bakin kokarinku a matsayinku na ‘yan kasuwa, amma ba wai kuna yin iyaka abun da ya dace ku yi ba kenan.

  • Shugaban Karamar Hukuma A Kano Ya Yi Murabus, Wani Kuma Ya Fice Daga APC Zuwa NNPP
  • Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta

“Dole mu hada karfi da karfe waje guda mu nemo mafita, a matsayina na gwam-na da mataimakina ba mu bukatar komai daga wajen kowa. Kawai abun da muke da bukata shi ne ku zo ku taimaka mana domin mu taimaki talakawanmu.”

Gwamna Yusuf ya bukaci ‘yan kasuwan da su taimaka wa kokarin gwamnatin ji-har, ya ce, “Ina rokonku da ku nemi hanyoyin rage farashin kayan masarufi domin saukaka wa jama’a.

“Kano cibiyar kasuwanci ce a Nijeriya baya ga Legas. Jihar tana samun kama-baya kowacce rana.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

“A baya, ‘yan kasuwa su na zuwa daga jihohin makwafta da ma kasashen waje domin yin sayayya a Jihar Kano, amma wannan lamarin na fuskantar tangarda.

“Manyan ‘yan kasuwan daga Nijar, Kamaru, Chadi da wasu sun maida Kano kamar gidansu. Amma a yau dukkaninsu sun canza. Sayan kayanmu ya ragu.

“Akwai damarmakin ayyukan yi sosai a Jihar Kano kuma akwai kamfanoni da daman gaske wadanda suke taimaka wa rayuwar al’umman. Sai dai a yanzu wasu sun zama tarihi. Wannan matsalar ya sanya matasa sun shiga harkokin shaye-shaye, garkuwa da mutane da fashin daji. Mutane su na rayuwa cikin tsananin ta-lauci, yayin da wasu ko mudun shinkafa ba su iya saye domin iyalansu su ci.

“Zan nemi ganin Shugaban kasa Bola Tinubu na shaida masa irin yunwar da ke addabar al’ummar Kano. Dole gwamnatin tarayya ta bayar da muhimmin tallafi ga jihar da ke da mutane masu tarin yawa.”

Wasu da suka yi magana a madadin ‘yan kasuwan kamar Alhaji Sabiu Bako, Alhaji Salisu Sambajo, Muhammad Adakawa, da Sammani Elsamad, gami da saura sun yi kira ga gwamna Yusuf da ya jagoranci sauran gwamnonin shiyyar arewa maso yamma domin nemo hanyoyin shawo kan matsalolin tattalin arziki da ke addabar al’ummar shiyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
cmg

An Nuna Dandanon Shirye-Shiryen Bikin Sabuwar Shekarar Sinawa Na CMG A Filin Jiragen Sama Da Yankunan Kasuwanci Na Dubai

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version