• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya zargi ‘yan Nijeriya da yin tsayuwar daka wajen amsar dukkanin wani abin da aka bijiro musu da shi walau mai kyau ko akasin hakan.

Ya nuna cewa wasu abubuwan sun bayyana wa ‘yan Nijeriya a zahirance, amma kuma suna ci gaba da rungumar abubuwa yadda suka zo a maimakon yin abin da ya dace.

  • Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman
  • CMG Da IOC Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Amaechi, wanda ya shiga harkokin siyasa a 1999 zuwa 2023, wanda ke magana a matsayin babban bako a taron lakca na shekara-shekara na TheNiche wanda ya gudana a cibiyar NIIA da ke Victoria Island a jihar Legas ranar Alhamis.

Duk da cewa an riga an bada rahoton abubuwan da suka wakana a wajen taron, sai dai a halin yanzu wani bidiyo mai tsawon mintina hudu na ci gaba da karade yanar gizo da ke kara daukar hankali.

A bidiyon, tsohon kakakin jihar Ribas kuma gwamnan jihar har sau biyu, ya bayar da dalilan da suka sanya ya yi gum da bakinsa, daga cikin dalilan har da cewa hadiminsa a bangaren yada labarai ya shawarcesa da ya yi shiru.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

“Akwai gidajen talabijin da daidaikun da suka yi ta samu na da cewa na yi magana kan batutuwa daban-daban tun lokacin da na bar ofis, amma na ki amincewa na yi maganar. Na ki yin hakan ne bisa dalilai guda biyu, na daya hadimina a bangaren yada labarai ya shawarce ni da kada na ce komai, ya fusata sosai da nake magana da ku.

“Na biyu, ‘yan Nijeriya ba su mayar da hankali kan komai ba. Abu saboda kawai da za a ce, ‘yan Nijeriya ba su kula kan komai, suna rungumar komai yadda ya zo musu. Akwai wani dan siyasa da ya taba ce muku shi ba barawo ba ne? wani dan siyasa ne ya halarci jami’a? wacce ‘yar siyasa ce ta ce muku ta yi hidimar kasa NYSC, sannan wani dan siyasa ne ya gaya muku yana da satifiket?”

Ya kara da nuni da cewa, duk da ‘yan Nijeriya sun san wasu ‘yan siyasar da ba su dace ba, amma har yanzu suna ci gaba da ba su dama.

“’Yan Nijeriya sun sani amma har yanzu suna ci gaba da zabarsu, don haka menene matsayarku? Don me ma zan yi magana alhali ba wani abu ne sabo ba? ‘yan Nijeriya su ne ke da damar zabin wanda suka aminta da wanda ba su gamsu da ba, ‘yan Nijeriya ke zaban wadanda za su zaba da wadanda ba za su zaba ba. Kai, koda ka je gidan dan Nijeriya ka kashe mahaifiyarsa, babbansa zai ci gaba da harkokin rayuwarsa. Babu wani abun da zai dameka, babu fa, don haka menene zai sa na tsaya bata lokacina?”

Tsohon ministan ya ce tun lokacin gwamnatin Jonathan zuwa ta Buhari an yi ta tafka muhawara da zuba maganganu sosai amma duk da haka jiya-i-yau don haka ne ya zabi ya zauna cikin gida ya ja bakinsa ya yi shiru kawai.

Ministan ya kara da cewa ‘yan Nijeriya ba su son gaskiya, har ma ya buga misali da cewa koda mutum ya fito ya ce musu shi karya yake musu ko kuma ya tafka wani laifin amma za su cigaba da amincewa da shi koda kuwa ya ma je gidan yari ya fito.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman

Next Post

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Related

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

4 hours ago
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

8 hours ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

11 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

22 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

1 day ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

1 day ago
Next Post
Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al'ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.