• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya zargi ‘yan Nijeriya da yin tsayuwar daka wajen amsar dukkanin wani abin da aka bijiro musu da shi walau mai kyau ko akasin hakan.

Ya nuna cewa wasu abubuwan sun bayyana wa ‘yan Nijeriya a zahirance, amma kuma suna ci gaba da rungumar abubuwa yadda suka zo a maimakon yin abin da ya dace.

  • Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman
  • CMG Da IOC Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Amaechi, wanda ya shiga harkokin siyasa a 1999 zuwa 2023, wanda ke magana a matsayin babban bako a taron lakca na shekara-shekara na TheNiche wanda ya gudana a cibiyar NIIA da ke Victoria Island a jihar Legas ranar Alhamis.

Duk da cewa an riga an bada rahoton abubuwan da suka wakana a wajen taron, sai dai a halin yanzu wani bidiyo mai tsawon mintina hudu na ci gaba da karade yanar gizo da ke kara daukar hankali.

A bidiyon, tsohon kakakin jihar Ribas kuma gwamnan jihar har sau biyu, ya bayar da dalilan da suka sanya ya yi gum da bakinsa, daga cikin dalilan har da cewa hadiminsa a bangaren yada labarai ya shawarcesa da ya yi shiru.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

“Akwai gidajen talabijin da daidaikun da suka yi ta samu na da cewa na yi magana kan batutuwa daban-daban tun lokacin da na bar ofis, amma na ki amincewa na yi maganar. Na ki yin hakan ne bisa dalilai guda biyu, na daya hadimina a bangaren yada labarai ya shawarce ni da kada na ce komai, ya fusata sosai da nake magana da ku.

“Na biyu, ‘yan Nijeriya ba su mayar da hankali kan komai ba. Abu saboda kawai da za a ce, ‘yan Nijeriya ba su kula kan komai, suna rungumar komai yadda ya zo musu. Akwai wani dan siyasa da ya taba ce muku shi ba barawo ba ne? wani dan siyasa ne ya halarci jami’a? wacce ‘yar siyasa ce ta ce muku ta yi hidimar kasa NYSC, sannan wani dan siyasa ne ya gaya muku yana da satifiket?”

Ya kara da nuni da cewa, duk da ‘yan Nijeriya sun san wasu ‘yan siyasar da ba su dace ba, amma har yanzu suna ci gaba da ba su dama.

“’Yan Nijeriya sun sani amma har yanzu suna ci gaba da zabarsu, don haka menene matsayarku? Don me ma zan yi magana alhali ba wani abu ne sabo ba? ‘yan Nijeriya su ne ke da damar zabin wanda suka aminta da wanda ba su gamsu da ba, ‘yan Nijeriya ke zaban wadanda za su zaba da wadanda ba za su zaba ba. Kai, koda ka je gidan dan Nijeriya ka kashe mahaifiyarsa, babbansa zai ci gaba da harkokin rayuwarsa. Babu wani abun da zai dameka, babu fa, don haka menene zai sa na tsaya bata lokacina?”

Tsohon ministan ya ce tun lokacin gwamnatin Jonathan zuwa ta Buhari an yi ta tafka muhawara da zuba maganganu sosai amma duk da haka jiya-i-yau don haka ne ya zabi ya zauna cikin gida ya ja bakinsa ya yi shiru kawai.

Ministan ya kara da cewa ‘yan Nijeriya ba su son gaskiya, har ma ya buga misali da cewa koda mutum ya fito ya ce musu shi karya yake musu ko kuma ya tafka wani laifin amma za su cigaba da amincewa da shi koda kuwa ya ma je gidan yari ya fito.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman

Next Post

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Related

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Nada Ɗan Babangida A Matsayin Shugaban Bankin Manoma

12 hours ago
Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Wani Harin Ta’addanci Tare Da Cafke Wasu Mutum Biyu A Taraba

17 hours ago
Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya
Manyan Labarai

Buhari 1942 – 2025: Rayuwarsa, Rasuwarsa, Jana’izarsa, Da Ci gaba Da Ta’aziyya

22 hours ago
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

1 day ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

1 day ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

2 days ago
Next Post
Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al'ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.