ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amaechi Ga ‘Yan Nijeriya: Akwai Dan Siyasar Da Ya Taba Ce Muku Shi Ba Barawo Ba Ne?

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Amaechi

Tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya zargi ‘yan Nijeriya da yin tsayuwar daka wajen amsar dukkanin wani abin da aka bijiro musu da shi walau mai kyau ko akasin hakan.

Ya nuna cewa wasu abubuwan sun bayyana wa ‘yan Nijeriya a zahirance, amma kuma suna ci gaba da rungumar abubuwa yadda suka zo a maimakon yin abin da ya dace.

  • Tun Ina Yarinya Ba Na So Na Ga Ana Zaman Banza -Rukayya Usman
  • CMG Da IOC Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa

Amaechi, wanda ya shiga harkokin siyasa a 1999 zuwa 2023, wanda ke magana a matsayin babban bako a taron lakca na shekara-shekara na TheNiche wanda ya gudana a cibiyar NIIA da ke Victoria Island a jihar Legas ranar Alhamis.

ADVERTISEMENT

Duk da cewa an riga an bada rahoton abubuwan da suka wakana a wajen taron, sai dai a halin yanzu wani bidiyo mai tsawon mintina hudu na ci gaba da karade yanar gizo da ke kara daukar hankali.

A bidiyon, tsohon kakakin jihar Ribas kuma gwamnan jihar har sau biyu, ya bayar da dalilan da suka sanya ya yi gum da bakinsa, daga cikin dalilan har da cewa hadiminsa a bangaren yada labarai ya shawarcesa da ya yi shiru.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

“Akwai gidajen talabijin da daidaikun da suka yi ta samu na da cewa na yi magana kan batutuwa daban-daban tun lokacin da na bar ofis, amma na ki amincewa na yi maganar. Na ki yin hakan ne bisa dalilai guda biyu, na daya hadimina a bangaren yada labarai ya shawarce ni da kada na ce komai, ya fusata sosai da nake magana da ku.

“Na biyu, ‘yan Nijeriya ba su mayar da hankali kan komai ba. Abu saboda kawai da za a ce, ‘yan Nijeriya ba su kula kan komai, suna rungumar komai yadda ya zo musu. Akwai wani dan siyasa da ya taba ce muku shi ba barawo ba ne? wani dan siyasa ne ya halarci jami’a? wacce ‘yar siyasa ce ta ce muku ta yi hidimar kasa NYSC, sannan wani dan siyasa ne ya gaya muku yana da satifiket?”

Ya kara da nuni da cewa, duk da ‘yan Nijeriya sun san wasu ‘yan siyasar da ba su dace ba, amma har yanzu suna ci gaba da ba su dama.

“’Yan Nijeriya sun sani amma har yanzu suna ci gaba da zabarsu, don haka menene matsayarku? Don me ma zan yi magana alhali ba wani abu ne sabo ba? ‘yan Nijeriya su ne ke da damar zabin wanda suka aminta da wanda ba su gamsu da ba, ‘yan Nijeriya ke zaban wadanda za su zaba da wadanda ba za su zaba ba. Kai, koda ka je gidan dan Nijeriya ka kashe mahaifiyarsa, babbansa zai ci gaba da harkokin rayuwarsa. Babu wani abun da zai dameka, babu fa, don haka menene zai sa na tsaya bata lokacina?”

Tsohon ministan ya ce tun lokacin gwamnatin Jonathan zuwa ta Buhari an yi ta tafka muhawara da zuba maganganu sosai amma duk da haka jiya-i-yau don haka ne ya zabi ya zauna cikin gida ya ja bakinsa ya yi shiru kawai.

Ministan ya kara da cewa ‘yan Nijeriya ba su son gaskiya, har ma ya buga misali da cewa koda mutum ya fito ya ce musu shi karya yake musu ko kuma ya tafka wani laifin amma za su cigaba da amincewa da shi koda kuwa ya ma je gidan yari ya fito.

Amaechi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Next Post
Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al’ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

Xi Jinping Ya Jaddada Muhimmancin Samar Da Kyakkyawar Fahimtar Al'ummantaka Ga Jama’ar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

Rundunar Sojin Ruwan Sin Ta Yi Gwajin Makami Mai Linzami Ta Amfani Da Jirgin Ruwa Mai Nutso

July 6, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Yi Ta’aziyyar ’Ya’yan Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi da Suka Rasu a Hatsarin Mota

July 6, 2026
An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

An Kaddamar Da Atisayen Hadin Gwiwa Mai Taken “Hadin Gwiwar Ayyuka Kan Teku-2026” Tsakanin Sin Da Rasha

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.