• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Da Walkiya Suka Haddasa Karancin Mai – NNPCL

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Kar Ku Tayar Da Hankulanku, Mun Samo Fetur Fiye Da Lita Biliyan 1.5 – NNPCL
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Man Fetur na kasa (NNPC Ltd.) ya danganta matsalolin karancin man fetur da ake a Babban Birnin Tarayya Abuja da wasu sassan kasar nan kan matsalar katsewar jigila sakamakon ambaliyar ruwa da wakkiya da ake samu a daminan bana.

Babban jami’in yada labarai na kamfanin, Mista Olufemi Soneye, shi ne ya sanar da hakan a ranar Litinin yayin da ke bayani kan matsalolin dogon layi da ake samu a gidajen mai.

  • Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-Zirga Ababen Hawa

Ya ce matsalar jigila daga manyan tashoshin kwaso mai zuwa kanana sakamakon ambaliyar ruwa da aka samu a baya-bayan nan shi ne musabbabin wannan matsala.

Soneye ya kuma ce rashin kyawun yanayi ya shafi hada-hadar jiragen ruwa, man-yan tankokin jigila, da kuma jigilar kayayyaki zuwa gidajen mai da suke sassa daban-daban na kasar nan, wanda hakan ya janyo cikas ga aikin samar da kayay-yakin ga gidajen mai.

“Kamfanin NNPC na son yin bayanin cewa saboda gudun tashin wutar fetur da kuma bin umarnin hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NIMET), hakan ya sanya ba za mu iya lodin man fetur a yanayin amfani da walkiya ba.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

“Bin wadannan dokoki da ka’idojin sun zama mana dole, duk wani tirjiya ga wadannan ka’idojin ka iya sanya a samu hatsari a cikin rayuwar mutane, motoci da gidajen mai.

“Matakin ya zama babban matsala ga jigilar motocin lodi daga wurin dibo mai zu-wa Babban Birnin Tarayya Abuja.

“Kamfanin NNPC Ltd, na aikin hadin guiwa da hukumomi da masu ruwa da tsaki wajen shawo kan matsalar kayan aiki da kuma yadda za a kauce wa mambaliyar ruwan domin ci gaba da jigilar mai a wuraren da lamarin ya shafa.

“Tuni aka ci gaba da aikin lodin mai a yankunan da ba su da irin wannan matsalar da kuma wadanda aka shawo kan yadda za a kauce wa matsalolin, kuma muna fatan za a ci gaba da samun sauki wajen daida komai cikin kankanin lokacin,” Soneye ya shaida.

Soneye ya gargadi gidajen mai da cewa kada su yi ganganci da motoci ko rayukan mutane wajen yin jigila a yanayin da bai da kyau, domin guje wa abun da ka iya je ya dawo.

A wannan lokaci dai an samu karancin mai da kuma dogon layuka a gidajen mai a wasu sassan kasar nan, lamarin da ya janyo wahalhalu ga jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuKarancin Man FeturSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

Next Post

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

1 hour ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

3 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

4 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

5 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

8 hours ago
Next Post
Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma'a Zuwa Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.