• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Da Walkiya Suka Haddasa Karancin Mai – NNPCL

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Kar Ku Tayar Da Hankulanku, Mun Samo Fetur Fiye Da Lita Biliyan 1.5 – NNPCL
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Man Fetur na kasa (NNPC Ltd.) ya danganta matsalolin karancin man fetur da ake a Babban Birnin Tarayya Abuja da wasu sassan kasar nan kan matsalar katsewar jigila sakamakon ambaliyar ruwa da wakkiya da ake samu a daminan bana.

Babban jami’in yada labarai na kamfanin, Mista Olufemi Soneye, shi ne ya sanar da hakan a ranar Litinin yayin da ke bayani kan matsalolin dogon layi da ake samu a gidajen mai.

  • Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-Zirga Ababen Hawa

Ya ce matsalar jigila daga manyan tashoshin kwaso mai zuwa kanana sakamakon ambaliyar ruwa da aka samu a baya-bayan nan shi ne musabbabin wannan matsala.

Soneye ya kuma ce rashin kyawun yanayi ya shafi hada-hadar jiragen ruwa, man-yan tankokin jigila, da kuma jigilar kayayyaki zuwa gidajen mai da suke sassa daban-daban na kasar nan, wanda hakan ya janyo cikas ga aikin samar da kayay-yakin ga gidajen mai.

“Kamfanin NNPC na son yin bayanin cewa saboda gudun tashin wutar fetur da kuma bin umarnin hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NIMET), hakan ya sanya ba za mu iya lodin man fetur a yanayin amfani da walkiya ba.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

“Bin wadannan dokoki da ka’idojin sun zama mana dole, duk wani tirjiya ga wadannan ka’idojin ka iya sanya a samu hatsari a cikin rayuwar mutane, motoci da gidajen mai.

“Matakin ya zama babban matsala ga jigilar motocin lodi daga wurin dibo mai zu-wa Babban Birnin Tarayya Abuja.

“Kamfanin NNPC Ltd, na aikin hadin guiwa da hukumomi da masu ruwa da tsaki wajen shawo kan matsalar kayan aiki da kuma yadda za a kauce wa mambaliyar ruwan domin ci gaba da jigilar mai a wuraren da lamarin ya shafa.

“Tuni aka ci gaba da aikin lodin mai a yankunan da ba su da irin wannan matsalar da kuma wadanda aka shawo kan yadda za a kauce wa matsalolin, kuma muna fatan za a ci gaba da samun sauki wajen daida komai cikin kankanin lokacin,” Soneye ya shaida.

Soneye ya gargadi gidajen mai da cewa kada su yi ganganci da motoci ko rayukan mutane wajen yin jigila a yanayin da bai da kyau, domin guje wa abun da ka iya je ya dawo.

A wannan lokaci dai an samu karancin mai da kuma dogon layuka a gidajen mai a wasu sassan kasar nan, lamarin da ya janyo wahalhalu ga jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuKarancin Man FeturSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

Next Post

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Related

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

2 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

4 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Manyan Labarai

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

4 hours ago
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro
Manyan Labarai

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

6 hours ago
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar
Manyan Labarai

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

7 hours ago
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

15 hours ago
Next Post
Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma'a Zuwa Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.