• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin baya aka yi bikin komawar wasu matasa ’yan Najeriya gida, bayan da kamfanin gine-gine na CCECC na kasar Sin ya dauki nauyin kwasa-kwasan samun kwarewa da suka kammala a kasar Sin a fannin aikin injiniyan jiragen kasa, da sauran fannoni masu nasaba da harkokin sufuri, matakin da ya yi matukar samun yabo daga sassa da dama.

Wannan kwazo na kamfanin CCECC karkashin manufarsa ta tallafawa al’ummun dake wuraren da yake gudanar da ayyuka, ya nuna yadda kamfanonin kasar Sin masu gudanar da manyan ayyukan samar da ababen more rayuwa ke sauke nauyin dake wuyansa na samar da ci gaba a duk inda suke ayyuka.

  • Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic
  • “ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin

Kaza lika, wannan tallafi da kamfanin ya samar ga dalibai ’yan Najeriya ya yi daidai da burin gwamnatin kasar na kara yayata shigar matasa ’yan kasar cikin harkokin sufurin jiragen kasa, kamar yadda hakan ke kunshe cikin manufar raya layukan dogo a Najeriya wadda gwamnatin kasar ta kaddamar a shekarar 2018.

Kamar dai yadda muke gani a nan kasar Sin, fannin sufuri ta layukan dogo ya zamo babban ginshiki dake taka rawar gani a bangaren kyautata rayuwar al’umma ta fuskoki da dama, wadanda suka hada da saukaka farashi da hidimomin zirga-zirga, dakon manyan hajoji, samar da guraben ayyukan yi da haraji, da kyautata amfani da makamashi mai tsafta a fannin sufuri da dai sauransu. Hakan na nufin idan irin wadannan manufofi na hadin gwiwa da tallafi daga kasar Sin suka dore, Najeriya da ma sauran sassan kasa da kasa musamman kasashe masu tasowa, za su amfana matuka daga fasahohin zamani na ci gaban sufuri ta layukan dogo.

Yanzu haka dai Najeriya na kan hanyar aiwatar da manufofin zamanintar da harkokin sufuri ta layukan dogo na tsawon shekaru 25, kuma za a aiwatar da hakan ne ta hanyar horas da matasa da za su rika samun kwarewa a aikace, don haka masharhanta da dama ke jinjinawa kamfanin CCECC bisa gudummawar kai tsaye da ya baiwa wannan manufa.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Ko shakka babu CCECC ya cancanci yabo, kuma tallafin kwarewa da ya samarwa wadannan matasa ’yan Najeriya, ya kara tabbatar da aniyar kasar Sin ta ci gaba da bunkasa hadin gwiwar moriyar juna da bangaren Najeriya, yayin da sassan biyu ke kara himmatuwa wajen zurfafa fahimtar juna, da fadada alakarsu daga dukkanin fannoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IOCIranRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Cibiyar Nuna Hadin Gwiwar Sin, Afrika Da MDD A Beijing

Next Post

Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

3 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

4 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

5 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

6 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

7 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

17 hours ago
Next Post
Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.