• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ’yan kwanakin baya aka yi bikin komawar wasu matasa ’yan Najeriya gida, bayan da kamfanin gine-gine na CCECC na kasar Sin ya dauki nauyin kwasa-kwasan samun kwarewa da suka kammala a kasar Sin a fannin aikin injiniyan jiragen kasa, da sauran fannoni masu nasaba da harkokin sufuri, matakin da ya yi matukar samun yabo daga sassa da dama.

Wannan kwazo na kamfanin CCECC karkashin manufarsa ta tallafawa al’ummun dake wuraren da yake gudanar da ayyuka, ya nuna yadda kamfanonin kasar Sin masu gudanar da manyan ayyukan samar da ababen more rayuwa ke sauke nauyin dake wuyansa na samar da ci gaba a duk inda suke ayyuka.

  • Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic
  • “ChinaTravel” Ya Fahimtar Da Al’ummar Duniya Hakikanin Yanayin Da Ake Ciki A Kasar Sin

Kaza lika, wannan tallafi da kamfanin ya samar ga dalibai ’yan Najeriya ya yi daidai da burin gwamnatin kasar na kara yayata shigar matasa ’yan kasar cikin harkokin sufurin jiragen kasa, kamar yadda hakan ke kunshe cikin manufar raya layukan dogo a Najeriya wadda gwamnatin kasar ta kaddamar a shekarar 2018.

Kamar dai yadda muke gani a nan kasar Sin, fannin sufuri ta layukan dogo ya zamo babban ginshiki dake taka rawar gani a bangaren kyautata rayuwar al’umma ta fuskoki da dama, wadanda suka hada da saukaka farashi da hidimomin zirga-zirga, dakon manyan hajoji, samar da guraben ayyukan yi da haraji, da kyautata amfani da makamashi mai tsafta a fannin sufuri da dai sauransu. Hakan na nufin idan irin wadannan manufofi na hadin gwiwa da tallafi daga kasar Sin suka dore, Najeriya da ma sauran sassan kasa da kasa musamman kasashe masu tasowa, za su amfana matuka daga fasahohin zamani na ci gaban sufuri ta layukan dogo.

Yanzu haka dai Najeriya na kan hanyar aiwatar da manufofin zamanintar da harkokin sufuri ta layukan dogo na tsawon shekaru 25, kuma za a aiwatar da hakan ne ta hanyar horas da matasa da za su rika samun kwarewa a aikace, don haka masharhanta da dama ke jinjinawa kamfanin CCECC bisa gudummawar kai tsaye da ya baiwa wannan manufa.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Ko shakka babu CCECC ya cancanci yabo, kuma tallafin kwarewa da ya samarwa wadannan matasa ’yan Najeriya, ya kara tabbatar da aniyar kasar Sin ta ci gaba da bunkasa hadin gwiwar moriyar juna da bangaren Najeriya, yayin da sassan biyu ke kara himmatuwa wajen zurfafa fahimtar juna, da fadada alakarsu daga dukkanin fannoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IOCIranRasha
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kaddamar Da Cibiyar Nuna Hadin Gwiwar Sin, Afrika Da MDD A Beijing

Next Post

Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

Related

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

5 hours ago
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

6 hours ago
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

7 hours ago
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

8 hours ago
Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
Daga Birnin Sin

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

9 hours ago
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

1 day ago
Next Post
Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.