• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa Da Walkiya Suka Haddasa Karancin Mai – NNPCL

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
12 months ago
in Labarai
0
Kar Ku Tayar Da Hankulanku, Mun Samo Fetur Fiye Da Lita Biliyan 1.5 – NNPCL
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamfanin Man Fetur na kasa (NNPC Ltd.) ya danganta matsalolin karancin man fetur da ake a Babban Birnin Tarayya Abuja da wasu sassan kasar nan kan matsalar katsewar jigila sakamakon ambaliyar ruwa da wakkiya da ake samu a daminan bana.

Babban jami’in yada labarai na kamfanin, Mista Olufemi Soneye, shi ne ya sanar da hakan a ranar Litinin yayin da ke bayani kan matsalolin dogon layi da ake samu a gidajen mai.

  • Kamfanin Kasar Sin Na Bayar Da Gudummawar Gani Wajen Bunkasa Kasar Najeriya
  • Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-Zirga Ababen Hawa

Ya ce matsalar jigila daga manyan tashoshin kwaso mai zuwa kanana sakamakon ambaliyar ruwa da aka samu a baya-bayan nan shi ne musabbabin wannan matsala.

Soneye ya kuma ce rashin kyawun yanayi ya shafi hada-hadar jiragen ruwa, man-yan tankokin jigila, da kuma jigilar kayayyaki zuwa gidajen mai da suke sassa daban-daban na kasar nan, wanda hakan ya janyo cikas ga aikin samar da kayay-yakin ga gidajen mai.

“Kamfanin NNPC na son yin bayanin cewa saboda gudun tashin wutar fetur da kuma bin umarnin hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NIMET), hakan ya sanya ba za mu iya lodin man fetur a yanayin amfani da walkiya ba.

Labarai Masu Nasaba

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

“Bin wadannan dokoki da ka’idojin sun zama mana dole, duk wani tirjiya ga wadannan ka’idojin ka iya sanya a samu hatsari a cikin rayuwar mutane, motoci da gidajen mai.

“Matakin ya zama babban matsala ga jigilar motocin lodi daga wurin dibo mai zu-wa Babban Birnin Tarayya Abuja.

“Kamfanin NNPC Ltd, na aikin hadin guiwa da hukumomi da masu ruwa da tsaki wajen shawo kan matsalar kayan aiki da kuma yadda za a kauce wa mambaliyar ruwan domin ci gaba da jigilar mai a wuraren da lamarin ya shafa.

“Tuni aka ci gaba da aikin lodin mai a yankunan da ba su da irin wannan matsalar da kuma wadanda aka shawo kan yadda za a kauce wa matsalolin, kuma muna fatan za a ci gaba da samun sauki wajen daida komai cikin kankanin lokacin,” Soneye ya shaida.

Soneye ya gargadi gidajen mai da cewa kada su yi ganganci da motoci ko rayukan mutane wajen yin jigila a yanayin da bai da kyau, domin guje wa abun da ka iya je ya dawo.

A wannan lokaci dai an samu karancin mai da kuma dogon layuka a gidajen mai a wasu sassan kasar nan, lamarin da ya janyo wahalhalu ga jama’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TinubuKarancin Man FeturSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Rikicin Tube Sarakuna Bala’i Ne Ga Arewa’

Next Post

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Related

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

3 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

4 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

6 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

6 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

7 hours ago
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Labarai

Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya

10 hours ago
Next Post
Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma’a Zuwa Lahadi

Za A Samu Ruwan Sama Da Guguwa A Nijeriya Daga Juma'a Zuwa Lahadi

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.