• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyo bayan bala’in ambaliya da ta addabi al’umomi da dama a kasar nan a cikin ‘yan kwanakin nan, Masarautar Jordan ta hannun wata kungiyar agaji ta Jordan Hashemite, ta bai wa Nijeriya tallafin kayayyakin agaji iri-iri. 

Kayayyakin da aka bayar a karkashin umarnin Sarki Abdullah na II bin Al-Hussein Al Hashimi na Kasar Jordan da rundunar sojojin sama ta Royal Jordan ta kai wa gwamnatin tarayya sun hada da kunshin kayan abinci da tufafi da barguna da kayan tsaftar jiki.

  • “Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa
  • Mu Masu Bin Dukkan Umurnin Kotu Ne —Shugaban INEC

A wata sanarwa da shugaban sashen yada labarai na hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), Manzo Ezekiel, ya fitar, ya ce wani jirgin saman Hercules C130 na rundunar sojojin sama na Masarautar Jordan da ke jigilar kayayyakin agajin ya isa bangaren dakon kaya na filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe, Abuja da misalin karfe 7: 45pm na daren Laraba.

Da yake karbar kayayyakin, a madadin gwamnatin tarayya, babban daraktan hukumar NEMA, Mustapha Habib Ahmed, ya yaba da irin wannan karamcin da Sarkin Jordan, da gwamnati da al’ummar Masarautar suka yi wa Nijeriya, musamman a halin da ake ciki a halin yanzu da ake ciki, don tallafa wa mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

Ahmed ya kuma mika godiyar shugaban kasa Muhammadu Buhari da ministar harkokin jin kai, Sadiya Umar Farouq bisa tallafin tare da bayar da tabbacin za a raba kayayyakin ga wadanda suka dace.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Mai magana da yawun tawagar da suka kai kayayyakin, Zeyed Mahmoud, ya ce sun dauki wannan mataki ne daga Sarkin Jordan domin tallafa wa wadanda ambaliyar ruwa ta shafa, kuma ya kasance tare da hadin gwiwar kasa da kasa da Nijeriya kan wannan iftila’i kasancewar kasashen biyu ‘yan uwan ​​juna ne.

Wakilinmu ya tattaro cewa babban daraktan hukumar ta NEMA ya samu hadin kai da wasu daraktocin hukumar wajen karbar tallafin.

Haka kuma a filin jirgin akwai jami’an hukumar Kwastam da hukumar shige da fice ta kasa (NIS) da sauran hukumomin da abin ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AgajiJordanKayan TallafiMasarautar JordanNEMA
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Mun Yi Allah-Wadai Da Kai Wa Ayarin Atiku Hari A Jihar Borno” —Dattawan Arewa

Next Post

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

Related

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

2 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

5 hours ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

6 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

8 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Next Post
Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

Karancin Man Fetur Ya Haddasa Tsadar Kayan Masarufi A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.