• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakiyar Shugaban Asusun bunkasa noma na kasa da kasa Katherine Meighan ta bayyana cewa, asusun ya taimaka wa wasu manoma a kasar nan da dala miliyan biyar.
Meighan ta ce, asusun ya bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gonarsu.

Mataimakiyar ta bayyana hakan ne lokacin wata ganawa ta musamamn da ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammad Mohmood Abubakar a Abuja wadda ta ce, asusun ya bayar da taimakon ne don tausaya wa manoman da iftila’in na ambaliyar ruwan ta shafa.

  • Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

“Mun bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata gonakinsu”.
Meighan ta jinjina wa gwamnatin kasar bisa zuba jarin da ta yi a harkar noma, musaman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma ci gaba da habaka fannin aikin nama a Nijeriya.

“A susun na kuma yin aikin kafada da kafada da gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke a cikin karkara”.

Ta kuma nuna jin dadinta bisa karin tallafin, musaman domin a kara habaka fannin aikin noma a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, asusun na kuma yin aikin kafada da kafada gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke karkara.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

A na sa jawabin ministan ya mika godiyasa a madadin gwamnatin tarayya a kan wannan tallafin kudaden, inda ya bayar da tabbacin cewa, gwamnatin za ta tabatar tallafin ya kai ga wadanda aka yi abin dominsu.

A wani labarain makamancin wannan kuwa, rahotannin da suka fito daga wasu jihohin kasar nan sun ce, iftila’in na ambaliyar ruwa ta kara janyo hauhawan farashin shinkafa da sauran amfanin gona.

An ruwaito wasu daga cikin manoman shugabanin kungiyar manoman masara sun sanar da cewa, mai yuwa farashin ya karu rashi, saboda da tsadar takin zamani da manoma suka fuskanta a daminar bana, inda suka yi kira ga sauran takwarorinsu kan su guje wa sayar da amfanin gonakarsu bana domin gudun kauwace wa faskantar matsala.

Sun yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar, gwamnatocin kasar nan, musamman gwamnatin tarayya da kawo masu dauki, musamman domin kar su durkushe a cikin fannin.

An ruwaito cewa, a yanzu haka dai a wasu kasuwannin da ke a kasar nan, musaman a jihar kaduna, buhun shinkafa mai nauyin kilo 100 ana sayar da shi naira 19,000 21,000.

Sai dai, kuma, farashin buhun waken soya ana sayar da shi kan naira 22,000 zuwa naira 24,000, inda buhun masara ya kai nira 16,000, kuma buhun farin wake, ana samun sa a kan 44,000 saboda ba a shiga kakarsa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An yi Kuskuren Ba Qatar Damar Karbar Bakuncin Kofin Duniya, Cewar Blatter

Next Post

Hukumar Zaɓe Ta Ce Babu Wani Binciken Laifi Da Suke Yi Wa Tinubu

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

1 month ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

1 month ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Faransa

Hukumar Zaɓe Ta Ce Babu Wani Binciken Laifi Da Suke Yi Wa Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.