• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Ambaliyar Ruwa: Manoma Sun Samu Tallafin Asusun Bunkasa Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakiyar Shugaban Asusun bunkasa noma na kasa da kasa Katherine Meighan ta bayyana cewa, asusun ya taimaka wa wasu manoma a kasar nan da dala miliyan biyar.
Meighan ta ce, asusun ya bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata amfanin gonarsu.

Mataimakiyar ta bayyana hakan ne lokacin wata ganawa ta musamamn da ministan noma da raya karkara, Dakta Mohammad Mohmood Abubakar a Abuja wadda ta ce, asusun ya bayar da taimakon ne don tausaya wa manoman da iftila’in na ambaliyar ruwan ta shafa.

  • Ambaliyar Ruwa: Kasar Jordan Ta Bai Wa Nijeriya Kayan Tallafi

“Mun bayar da kudin ne ga gwamnatin kasar domin a tallafa wa manoman da ambaliyar ruwa ta lalata gonakinsu”.
Meighan ta jinjina wa gwamnatin kasar bisa zuba jarin da ta yi a harkar noma, musaman domin a kara samar da wadataccen abinci da kuma ci gaba da habaka fannin aikin nama a Nijeriya.

“A susun na kuma yin aikin kafada da kafada da gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke a cikin karkara”.

Ta kuma nuna jin dadinta bisa karin tallafin, musaman domin a kara habaka fannin aikin noma a fadin kasar nan, inda ta kara da cewa, asusun na kuma yin aikin kafada da kafada gwamnatin kasar nan, musamman kan yadda za a mayar da hankali matuka a kan kananan manoman da ke karkara.

Labarai Masu Nasaba

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

A na sa jawabin ministan ya mika godiyasa a madadin gwamnatin tarayya a kan wannan tallafin kudaden, inda ya bayar da tabbacin cewa, gwamnatin za ta tabatar tallafin ya kai ga wadanda aka yi abin dominsu.

A wani labarain makamancin wannan kuwa, rahotannin da suka fito daga wasu jihohin kasar nan sun ce, iftila’in na ambaliyar ruwa ta kara janyo hauhawan farashin shinkafa da sauran amfanin gona.

An ruwaito wasu daga cikin manoman shugabanin kungiyar manoman masara sun sanar da cewa, mai yuwa farashin ya karu rashi, saboda da tsadar takin zamani da manoma suka fuskanta a daminar bana, inda suka yi kira ga sauran takwarorinsu kan su guje wa sayar da amfanin gonakarsu bana domin gudun kauwace wa faskantar matsala.

Sun yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar, gwamnatocin kasar nan, musamman gwamnatin tarayya da kawo masu dauki, musamman domin kar su durkushe a cikin fannin.

An ruwaito cewa, a yanzu haka dai a wasu kasuwannin da ke a kasar nan, musaman a jihar kaduna, buhun shinkafa mai nauyin kilo 100 ana sayar da shi naira 19,000 21,000.

Sai dai, kuma, farashin buhun waken soya ana sayar da shi kan naira 22,000 zuwa naira 24,000, inda buhun masara ya kai nira 16,000, kuma buhun farin wake, ana samun sa a kan 44,000 saboda ba a shiga kakarsa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An yi Kuskuren Ba Qatar Damar Karbar Bakuncin Kofin Duniya, Cewar Blatter

Next Post

Hukumar Zaɓe Ta Ce Babu Wani Binciken Laifi Da Suke Yi Wa Tinubu

Related

Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

2 days ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

1 week ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

1 week ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Nijeriya Daga Faransa

Hukumar Zaɓe Ta Ce Babu Wani Binciken Laifi Da Suke Yi Wa Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.