• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Na Ci Gaba Da Cin Kare Ba Babaka A Kasar Syria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka ta sanar da janye jiki daga kasar Syria tun shekaru 4 da suka wuce, amma har zuwa yanzu, wasu sojojin kasar Amurka 900 na ci gaba da kasancewa a arewacin kasar.

A cewar kasar Amurka, dalilin da ya sa hakan shi ne magance farfadowar kungiyoyin masu tsattsauran ra’ayi a Syria. Amma a cewar gwamnatin kasar Syria, wadannan sojoji na kasar Amurka na kwatan danyen mai, da alkama, da sauran albarkatu iri-iri na kasar.

  • Bai Kamata Amurka Ta Kara Fadawa Hanyar Da Ba Ta Dace Ba

Hakika wani babban aiki na wadannan sojojin kasar Amurka, shi ne samar da goyon baya ga dakarun kasar Syria masu kin jinin gwamnati, inda ake ba su taimako wajen mallakar mahakan mai da iskar gas dake arewa maso gabashin kasar, da jigilar mai zuwa kasar Iraki domin sayar da shi.

A cewar gwamnatin kasar Syria, sojojin Amurka da dakaru masu kin jinin gwamnati, sun riga sun haddasa mata asarar da ta kai dalar Amukra biliyan 25.9. Kana a watanni 6 na farko na shekarar bana, sojojin Amurka da dakarun da suke samun goyon baya daga wajensu, sun kwaci fiye da kaso 80 na danyen man da aka haka a kasar Syria.

Ban da wannan kuma, kasar Amurka da wasu kawayenta na ci gaba da saka takunkumi kan kasar Syria, ko da yake kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya bai samar da iznin yin haka ba. Wannan takunkumi ya shafi bangarorin tattalin arzikin kasar Syira masu muhimmanci, da suka hada da danyen mai, da wutar lantarki, da cinikayya, da dai sauransu, lamarin da ya haddasa raguwar kudin shigar da jama’ar kasar suke samu, da hauhawar farashin kaya.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Zuwa yanzu kashi 90% na al’ummar kasar sun tsunduma cikin kangin talauci. Kana daga shekarar 2019 har zuwa yanzu, matsakaicin farashin kayayyaki na kasar ya karu da kashi 800%. Kuma wani abun takaici shi ne, Amurka da kawayenta sun ce dalilin da ya sa suka kakaba wa kasar Syria takunkumi shi ne kare jama’ar kasar.

Hakika Amurka ba za ta daina yin tasiri a kasar Syria ba. Ta hanyar raunana gwamnatin Syria da takunkumi, da taimakawa dakaru masu kin jinin gwamnati da damar shawo kan albarkatun danyen mai da iskar gas, kasar Amurka na ci gaba da kokarin neman hambarar da gwamnatin kasar. Ko da yake tana gudanar da ayyukan fakewa da kalmomin “dimokuradiya”, da “hakkin dan Adam”, da “tsaro”, da “zaman lafiya”. Amma kar mu manta, cikin shekaru 20 da suka wuce, matakan da kasar Amurka ta dauka a kasashe da yankuna 85, sun haddasa asarar rayukan mutane kimanin dubu 900, da rashin matsugunan mutane fiye da miliyan 38.

Tutocin “Dimokuradiyya”, da “Hakkin dan Adam” da kasar Amurka ta rike sun riga sun lallata sosai. Anya kasar za ta iya ci gaba da fakewa da su? (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan AS’HABUL KAHFI Za Su Daukaka Kara Kan Hukuncin Kisa Ga Abduljabbar

Next Post

Masu Garkuwa Sun Kashe ‘Yan Gida Ɗaya Bayan Sun Karɓi Kudin Fansarsu Naira Miliyan 60

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

13 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

14 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

16 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

17 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

24 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Sace Yara 3, Sun Bukaci Kudin Fansa Naira Miliyan 100 A Jihar Kogi

Masu Garkuwa Sun Kashe 'Yan Gida Ɗaya Bayan Sun Karɓi Kudin Fansarsu Naira Miliyan 60

LABARAI MASU NASABA

Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.