• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

by Khalid Idris Doya
3 months ago
in Rahotonni
0
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Amurka ta sayi kayayyakin da darajarsu ya kai dala miliyan 643.1 daga Nijeriya a farkon watanni biyu na 2025, wata guda kafin fara aiwatar da dokar haraji ta gwamnatin Shugaba Trump.

Dokokin harajin wanda ta fara aiki daga ranar 9 ga Afrilun 2025, ya sanya masu ruwa da tsaki na nuna damuwa kan irin tasirin da tsare-tsaren harajin za ta iya yi ga kasuwannin Nijeriya.

  • Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba
  • Sin Ta Bayyana Wani Shiri Na Bunkasa Kiwon Lafiya

Ko da yake, an tsame bangare mai da ma’adinai daga sabon tsarin harajin, lamarin da ya dan kawo sauki ga Nijeriya.

Bayanai daga hukumar kasuwancin kasa da kasa ta Amurka na cewa kayan da aka shigo da su daga Nijeriya a watan Fabrairun 2025 ya kai na dala miliyan 286.3, inda ya samu koma-baya ga dala miliyan 423.6 da aka samu a irin wannan lokaci na shekarar da ta gabata.

Jimillar cinikayya tsakanin Amurka da Nijeriya na watanni biyu na farkon shekarar 2025 ya kai kusan dala biliyan 1.33.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Wannan ya hada da darajar kayayyakin da ake shigowa da su daga waje da kuma fitar da su, wanda ke nuni da irin dimbin alakar kasuwanci da ke tsakanin kasashen biyu.

Kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa a cikin gida da na waje da jirgin ruwa ya kai dala miliyan 473.6 a watan Fabrairun 2025, kadan ya ragu daga dala miliyan 501 a watan Fabrairun 2024, wanda ke nuna raguwar kashi 5.5 cikin dari.

A shekarar zuwa yau, fitar da kayayyaki na FAS ya ragu daga dala miliyan 792.8 a shekarar 2024 zuwa dala miliyan 687.4 a shekarar 2025, wanda ya nuna raguwar kashi 13.3 cikin dari.

Amurka ta samu gibin ciniki a kan Nijeriya ne kawai a watan Janairun 2025, kamar yadda rahoton cinikayyar kayayyaki ta Amurka ya nuna.

Rahoton ya nuna cewa Amurka ta yi gibin dala miliyan 143 a watan Janairu amma ta samu rarar dala miliyan 187 a watan Fabrairu. Wannan ingantaccen canji ya haifar da rarar dala miliyan 44 a kowace shekara.

Bayanai sun nuna cewa kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa zuwa Amurka sun habaka sosai a watan Fabrairu, wanda ya kai dala miliyan 474 idan aka kwatanta da dala miliyan 214 da aka fitar a watan Janairu.

A wani labarin kuma, Ministan Kudi na Nijeriya da Harkokin Tattalin Arziki, Wale Edun, ya ce harajin kashi 14 cikin 100 na baya-bayan nan da Amurka ta kakaba kan kayayyakin da Nijeriya ke fitarwa zuwa kasashen waje zai yi wa tattalin arzikin Nijeriya illa.

Edun ya bayyana haka ne a taron kaddamar da harkokin mulki na kamfanoni da ma’aikatar kudi ta kasa ta shirya a Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaKayayyakiNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Na Dauki Karramawar Jaridar LEADERSHIP Da Matukar Muhimmanci – Gwamna Abba

Next Post

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

3 weeks ago
Amurka
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 month ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 month ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

1 month ago
Next Post
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final

July 6, 2025
Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

Chelsea Ta Kammala Ɗaukar Jamie Gittens Daga Borussia Dortmund

July 6, 2025
Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

Tsoro, Fargaba Da Wahala: ‘Bala’in Da Muka Gani A Yakin Sudan

July 6, 2025
Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

Bayern Munich Ta Fara Zawarcin Marcus Rashford

July 6, 2025
Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

July 6, 2025
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.