ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Nuna Kwarewa Da Gogewa A Sha’anin Mulkin Nijeriya – Bishir Dauda

by Bello Hamza
6 months ago
Tinubu

A karshen makon jiya ne Editanmu Bello Hamza ya tattauna da Kwamared Bishir Dauda a kan halin da kasa ke ciki da kuma yadda yake ganin shugaban kasa Bola Tinubu ke tafiyar da mulkin Nijeriya, musamman yadda yake tunkarar matsalalolin tsaro da kuma tsangwamar da Amurka ke yi mana a kan zargin yi wa Kiristoci kissan kare dangi. Ga dai yadda hirar ta kasance.

Za mu so ka gabatar mana da kanka

  • Wang Yi Ya Zanta Da Ministocin Wajen Cambodia Da Thailand 
  • FIFA Za Ta Bayar Da Dala Miliyan 50 Ga Kasar Da Ta Lashe Gasar Cin Kofin Duniya

Sunana Kwamared Bishir Dauda Sabuwar Unguwa Katsina, dan rajin kare Dimokaradiyya, hakkin dan Adam da ganin dunkulewar kasashen Afirika. Ina jagorantar kungiyar farar hula mai suna ‘Citizens Participation Against Corruption Initiatibe’, kuma nine babban sakataren Kungiyar Muryar Talaka a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Kwanan nan Shugaba Tinubu ya sanya dokar-ta-baci a bangaren tsaro a kasar nan, wani karin bayani zaka yi a kan haka.

Shugaba Tinubu yana ta kara ba makiyan Nijeriya mamaki. Yana nuna kwarewa da gogewa a sha’anin mulki fiye da tunanin duk mai tunani. Sanya dokar ta-baci sako ne ga makiyan Nijeriya na cikin gida da na waje cewa gwamnati ba barci take ba. Kuma shugabanninmu ba su rude ba. Suna daukar matakai dalla-dalla don tunkarar kowane irin kalubale ko barazana da ke fuskantar kasar nan. Kada ka manta kasarmu na fuskantar barazana daga shugaban wata kasar waje wadda keda tarihin yi wa kasashe katsa-landan. Amerika karkashin Donald Trump ta samu matsala. Ba su girmama dawaici da mutuncin wasu kasashe. Sannan Donald Trump babu ruwan shi da dokokin kasashen duniya, babu difilomasiyya ko dattako a harkar shi don haka dole shugaba Tinubu ya ayyana dokar ta-baci. Fatanmu shi ne jami’an tsaronmu a daidai wannan mawuyancin hali da muke ciki za su nuna matukar kishin kasa ta hanyar nuna sadaukarwa. Su yi koyi da takwarorin su na kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso wanda suke aiki da kishin kasa ba tare da nuna gazawa ba.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Yakamata ‘yan siyasa masu siyasa da tsoro da su daina. Nijeriya ce farko kafin siyasa. Sai akwai Nijeriya kafin a yi siyasa.

Haka muma farar hula ya kamata mu saita kanmu. Yanzu muna fuskantar wani irin kalubale, to ya kamata mu hada kai da gwamnati mu kare mutuncin kasarmu. Jayayya a daidai wannan lokacin hadari ce mu guje ta.

‘Yan Nijeriya da dama sun yaba da nadin Janar CG Musa a matsayin Ministan Tsaro. Wani tasiri kake ganin haka zai kara wa harkar samar da tsaro a Nijeriya?

Shugaba Tinubu ya jefi tsuntsaye da yawa da dutsi daya. Na farko ya rufe bakin ‘yan ta tarwatse masu cewa ana ma Kiristoci kisan gilla. To yanzu Kirista ne Ministan Tsaro. Zai yiwu Ministan Tsaro Kirista ya bari ana ma ‘yan uwanshi kiristoci kisan gilla? Na biyu, Shugaba Tinubu ya rufe bakin masu cewa yakamata a nada tsohon soja a matsayin Ministan Tsaro. To yanzu ga shi ya nada tsohon soja a wannan mukami. Na uku, nadin CG Musa kariya ce ga gwamnatin da mulkin Dimokaradiyya, idan mu kai la’akari da yadda sojoji ke hambarar da gwamnatoci a kasashen Afirika. CG Musa ya san sojoji, yasan matsalolinsu don haka, yana da ilimin abin da zai dakike duk wani yunkuri da za a iya yi don illata Dimokaradiyya. Idan ka hada da tsaffin sojojin da Tinubu ya nada jakadoji, yanzu gwamnatin na cike da sojoji ta yadda an kara rufe bakin masu ganin sojoji nada hujjar yin kutse.

To sai dai CG Musa ba zai iya samun cikakkiyar nasara ba, sai ya yi aiki hannu da hannu tare da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan Tsaro, dama gwamnoni. Maganar ba zai tattauna da ‘yan ta’adda ba, yakamata ya je yai shawara da sauran masu ruwan da tsaki.

Wani kira kake da shi ga al’ummar Nijeriya na su ba gwamnati goyon baya don samun nasarar samar da tsaro a fadin kasar nan?

Gani ga wane ya ishi wane tsoron Allah. Yanzu an yo walkiya an ga kowa. Masu kai kasarmu kara zuwa ga Amerika da kiran ta kawo mamu hari, suna da sauran mantuwa. Watakila basu ma bibiyar abubuwan da ke faruwa a duniya. Babu wata kasa da za ta iya gyara Nijeriya. A tarihi ba a taba samun wata kasa ta je ta gyara wata kasa ba. Kila hakan yasa mutanen kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso suka kori sojojin kasashen Yamma. Duk wanda yake tunanin Amerika za ta zo ta taimakai to bai ma fahimci Amerika ba. Hawan Donald Trump, Amerika ta soke hukumar I SAID mai bada tallafi. Ta soke tashar rediyon Hausa ta BOA, ta soke shirin AGOA, sannan Amerika ta koma tana lafta wa kasashenmu harajin cinikayya. To Yaya me yin haka zai taimake ka in banda batan basira?

Mu hada kai da gwamnati ya zama wajibi. Mun ga yadda ‘yan Nijar suka hada kai da gwamnatin mulkin soja suka hana kungiyar ECOWAS katabus. To in har wasu duk da mugunta irin ta mulkin soja, amma saboda kishin kasa, za su hada kai da sojan, me zai sa muda keda shugaba adali wanda muka zaba ba za mu hada kai da gwamnati ba?

Ko akwai wani bayani da kake son yi wa al’umma wanda bamu tabo ba?

Yakamata ‘yan Nijeriya mu kalli baiwar da Allah ya yi mana, mu gode mai, mu so kasarmu. Mu daina kira wa kanmu ruwa. ‘Yantawaye da masu tada tarzoma su daina. Ba in da tsiya da bindiga za sui kai mutum. Duk irin rashin mutuncin mutum kafin shi an taba wani, Kuma Allah ya kauda shi. Saboda haka mu bi a hankali mu saita kasarmu. Kada mu yarda mu raba kawunanmu, kasashe ‘yan mamaya su samu damar cimmamu.

 

Mun gode kwarai da gaske

Nima na gode

Tinubu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.