• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Amurka Tana Murnar Mummunar Ribar Da Ta Ci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Amurka da kamfanonin samar da makaman soja na kasar sun kara cin mummunar riba.

A ranar 29 ga wata, ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Amurka ta bayar da sanarwar cewa, a shekarar 2023, kudin makaman soja da ta sayar ga kasashen ketare ya karu da kaso 16%, adadin da ya kai har dalar Amurka biliyan 238. Kafin wannan, alkaluman da cibiyar nazari ta SIPRI da ke birnin Stockholm ta samar sun shaida cewa, daga shekarar 2018 zuwa ta 2022, yawan makaman da kasar Amurka ta fitar zuwa ketare ya dau kaso 40% na dukkanin makaman da aka fitar a fadin duniya, adadin da ya karu da kashi 7% bisa na tsakanin shekarar 2013 da ta 2017.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Rangadi A Tianjin 
  • Karuwar Rincabewar Tsaro: Manyan Hafsoshi Sun Shiga Tsaka Mai Wuya

Hakan ya faru ne sakamakon yadda Amurka ta yi ta rura rikici a fadin duniya don cin mummunar riba, matakin da ya lalata zaman lafiya a duniya. Rahoton da cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka ta fitar ya yi nuni da cewa, daga shekarar 2012 zuwa ta 2022, Amurka ta sayar da manyan makamai da kudinsu ya kai dala biliyan 16 ga kasashe da shiyyoyi 28 da ke fama da rikici a duniya. Bayan barkewar rikici tsakanin Palasdinu da Isra’ila a wannan karo, Amurka ba ma kawai ta gaggauta samar da gudummawar soja ga Isra’ila ba, har ma ta sayar da makaman soja ga Isra’ila din har sau biyu a watan Disamban bara, kuma ba tare da an tattauna batun a majalisar dokokin kasar ba. Ban da haka, a bara, Amurka ta ci gaba da rura wutar rikicin Ukraine. Tun bayan barkewar rikicin a watan Faburairun shekarar 2022, Amurka ta riga ta samar da gudummawar da ta zarce dala biliyan 110 ga Ukraine din. A shirin kasafin kudi na bana da gwamnatin Biden ta gabatar, an ware dala biliyan 106 ta fannin samar da gudummawar soja ga Isra’ila da Ukraine da sauransu.

Sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana a fili cewa, “A hakika kaso 90% na kudin gudummawar soja da muka samarwa Ukraine, an kashe su ne a cikin gidan Amurka, ta fannonin masu samar da kayanmu, kuma hakan ya kara samar da guraben aikin yi ga Amurkawa, tare da sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikinmu.” To, dalili ke nan da ya sa Amurka ke matukar sha’awar tada rikci a duniya.

Ba da jimawa ba bayan barkewar rikicin Ukraine, mista Franklin C. Spinney wanda ya shafe shekaru da dama yana aiki a ofishin ministan tsaron kasar Amurka ya rubuta cewa, rikicin Rasha da Ukraine “ya sa mutane da yawa a ma’aikatar tsaron kasar Amurka ta Pentagon da masana’antun samar da makamai na kasar da ma majalisar dokokin kasar sun taya juna murna asirce. ” Abin haka yake, abin da ke faruwa a kasashen da ke fama da rikici, ba kome ba ne ga ‘yan siyasar kasar Amurka da ma sojoji da masana’antun samar da makamai na kasar, sabo da mummunar riba mai tsoka da suka ci. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasar Sin Ya Yi Rangadi A Tianjin 

Next Post

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

4 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

1 day ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

2 days ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

1 week ago
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Ra'ayi Riga

Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba

2 weeks ago
Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
Ra'ayi Riga

Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya

2 weeks ago
Next Post
Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

Cire Tallafin Man Fetur: Minista Ya Yaba Wa IPMAN Don Rungumar Shirin CNG

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.