ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karuwar Rincabewar Tsaro: Manyan Hafsoshi Sun Shiga Tsaka Mai Wuya

by Bello Hamza and Yusuf Shuaibu
2 years ago
Manyan Hafsoshi

Lamarin tsaro a ‘yan kwanakin nan sun kara rincabewa, wanda hakan ya sa shugabannin rundunonin tsaro shiga tsaka mai wuya, inda al’umma ke neman karin bayani wasu kuma suna ganin jami’an tsaron basu tabuka komai ba ganin irin dinbin kudaden da ake zubawa a bangaren tsaro a kasar nan.

A kan haka ne majalisar dattawa ta gayyaci shugabanin rundunonin tsaron zuwa zauren majalisar don tattaunawa tare da nemo bakin zare.

  • Zaben Cike Gurbin Makera: ‘Yan Takara Sun Yi Wa Liman Mubaya’a
  • Matsalar Tsaron Nijeriya: Ku Faɗi Alkairi Ko Ku Yi Shiru!

Haka kuma majalisar wakilai ta yanke shawarar ganawa da Shugaban Kasa Bola Tinubu ganin yadda ake samun karuwar hare-haren ta’addanci da garkuwa da mutane a sassan kasar nan a cikin makon jiya, musamman ma hare-haren da aka kai yankin karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato inda mutum fiye da 50 suka mutu yayin da aka tabbatar da mutum 100 sun ji munanan raunuka, an kuma kona gidaje masu yawan gaske, an kuma tabbatar da rikicin ya tarwatsa mutane fiye da 20, 000 daga gidajensu, a halin yanzu suna sansanonin gudun hijira a sassan jihar.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran babban hafsan tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa; Shugaban rundunar sojin Nijeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja; Shugaban Sojojin Sama, Air Marshal Hassan Abubakar; Shugaban Sojojin Ruwan Nijeriya, Cif of Nabal Staff (CNS), da kuma shugaban rundunar sojojin sama, Bice Admiral Emmanuel Ogalla sai kuma Sufeton ‘Yan Sandan Nijeriya Kayode Adeolu Egbetokun su bayyana a gaban majalisar inda za su bayyana wa ‘yan majalisar irin kokarinj da suke yi na magance matsalar tsaron da kuma dalilan da ya sa har yanzu abin ya-ki ci ya-ki cinyewa.

A mako mai zuwa ne za su gurfana a gaban majalisar bayan ‘yan majalisar sun dawo daga hutun mako daya da suka tafi don shiga harkokin zaben cike gurbi da za a yi a fadin kasar nan a ranar Asabar.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A kudurin da aka gabatar don gayyatar shugabanin rundunomin tsaron wanda ‘yan majalisar dattawa 109 suka sanya wa hannu sun bayyana damuwar su a kan yadda ayyukan ‘yan bindiga da kashe-kashe, da garkwua da mutane da sauran ayyukan ta’addanci suka mamaye sassan kasar nan.

Majalisa ta kuma lura da yadda ayyukan ‘yan ta’adda suka kara ta’azzara a yankin babban birnin tarayya Abuja, musamman garkuwa da mutaned da neman kudin fansa, inda sakamakon haka aka kashe mutane da dama haka kuma sun lura da yadda aka kashe wasu sarakuna gargajiya biyu a Jihar Ekiti da kuma yadda aka sace malamai da ‘yan makaranta a garin Ekiti, da kuma sauran ayyukan ‘yan ta’adda a sassan Nijeriya.

– Ana Samun Nasara A Kan Miyagun -Gwamnati
Yayin da ka yi garkuwa da wasu malaman makaranta da dalibansu a jihar Ekiti, al’umma sun harzuka inda suke nemi gwamnati ta dauki matakin gaggwa don kawo karshen lamarin. A kan haka ne shugaban kasa Bola Tinubu ya umarci a gagguta ceto malaman da daliba ba tare da bata lokaci ba.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin mai magana da yawun shugaban kasan, Ajuri Ngelale, inda ya kara da cewa, Tinubu ya tabbatar wa da al’umma cewa, a halin yanzu ana yi wa tsarin rundunonin tsaron kassar nan garambawul ta yadda za su yi aiki yadda ya kamata.

Haka kuma shugaban kasa Tinubu ya tir da yadda aka kashe sarakuna gargajiya biyu a Jihar Ekiti, sarakuna syun hada da Onimojo na Imojo-Ekiti, Oba Olatunde Samuel Olusola, da kuma Elesun na Esun-Ekiti, Oba Dabid Babatunde Ogunsola.

Tinubu ya yi tir da kashe kashen da ake tafkawa ya kuma yi alkawarin tabbatar da hukunta wadanda suke aikata wadannan ta’asar. Ya ce, duk da mastalolin da ake fuskanta ana samun nasara a kan ‘yan ta’adda, kuma da sannu za a yi galaba a kan su.

– Masu Garkuwa Na Neman Fansar Naira Miliyan 100
A halin yanzu masu garkuwa da malamai da daliban da aka sace a Jihar Edkiti sun nemi a biya su diyyar naira miliyan 100 kafin su saki yaran da suka sacen.

Majiya na kusa da iyalan daliban suka bayyana wa ‘yan jarida a tattaunawarsu da manema labarai, sun ce masu garkwua na neman naira miliyan 10 a kan kowanne dalibi.

– Atiku Ya Sake Caccakar Tinubu
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya caccaki Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu kan gazawa wajen magance matsalar tsaro. Ya bukaci ya jefar da kwallon mangwaro domin ya huta da kuda.
Atiku ya kasance dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar PDP a zaben 2023, ya dai bayyana takaicinsa ta yadda ake samun karuwar garkuwa da mutane da kuma kasha-kashe a ko’ina a fadin kasar nan.
Ya dai yi takaicin yadda aka kashe wata matashiya tare da mahaifiyarta a Abuja da kuma kisan sarakuna biyu a Jihar Ekiti a ranar Litinin.

Tsohon mataimakin shugaban kasan ya yi mamakin yadda shugaban kasa ya jilla zuwa kasar Faransa ba tare da daukar mataki kan ‘yan bindiga da kuma sauran ayyukan ta’addanci da ke faruwa a kasar nan.

A dai ranar Laraba da ta gabata ce, Shugaban kasa Tinubu ya zai ziyara ta musamman a kasar Faransa.
A shafinsa na sada zumunta, Atiku ya rubuta cewa, “Tinubu bai damu da halin da Nijeriya ke ciki ba na rashin tsaro. Abun mamaki fa shi ne babban kwamandar askarawan kasar nan, amma har zai iya yin wata ziyara ta musaman a wannan yanayi da ake fama da rashin tsaro a Nijeriya.

“A daidai wannan lokaci, masu garkuwa da mutane sun kashe wata matashiyar likita tare da kakarta a Abuja sakamakon gaza biyan kudin fansa na naira miliyan 90. Sannan sun kashe sarakuna guda biyu a Jihar Ekiti, dadai sauran ‘yan Nijeriyan da aka kashe da bazan iya lissafawa ba.
“Idan har matsalar ta gagare ka ne, to ka kama gife akwai masu iyawa. A halin yanzu ‘yan Nijeriya ba sa bukatar shugaba mai son shakatawa.

“Kasar nan na bukatar shugaban da zai iya aiki na tsawon awanni 24 na kowacce rana, domin magance rashin tsaro da kuma durkushewar tattalin arziki.”

– Yadda Lamarin Yake A Arewa
Masu garkuwa da mutanen sun yi awon gaba da dan matan biyu masu shekara 16 da 14 a Kubwa da ke karamar Hukumar Bwari, birnin tarayya Abuja.

Sun nemi mahaifin yaran da ya ba su Naira miliyan 30 idan har yana son yaransa su shaki iskar ‘yanci.
Lamarin dai ya faru ne a ranar Talata da misalin karfe 11:25 na dare.

Manyan Hafsoshi
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Amfani Da Matar Soja Wajen Isar Da Sakon Bukata
Manyan Hafsoshi
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yajin aiki

Muna Bin ‘Yan Bindiga Har Maboyarsu Mu Fatattake Su - Minista

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.