• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka Za Ta Lashe Amanta Game Da Karin Harajin Rashin Adalci Da Ta Bugawa Kasar Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Amurka Za Ta Lashe Amanta Game Da Karin Harajin Rashin Adalci Da Ta Bugawa Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata 14 ga watan nan ne gwamnatin Amurka, ta sanar da buga karin haraji kan wasu hajojin dake shiga kasar daga kasar Sin, matakin da ya gamu da nuna rashin jin dadi, da adawa daga al’ummar duniya. 

Amurka ta rika siyasantar da batun ciniki, wanda hakan ya keta hurumin hada-hadar cinikayyar sassan biyu, kuma zai illata bunkasuwar harkoki masu alaka, daga karshe dai Amurka za ta lashe amanta tare da gamu da babbar illa.

  • Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
  • Shugabannin Sin Da Rasha Sun Tattauna Da Juna

Hajojin da gwamnatin Amurka ta dorawa matsin lamba a wannan karo sun shafi musamman na fannin amfani da makamashi mai tsabta. Sakamakon haka muna iya ganin cewa, zargin da wasu manyan jami’an Amurka suka yi, cewar wai yawan hajoji masu aiki da makamashi mai tsabta da Sin ke samarwa sun wuce misali, hujja ce kawai ta neman buga karin haraji.

To ko mene ne dalili? Manazarta na ganin cewa, a wani bangare, Amurka ta gaza samun karfin takara a wannan bangare, shi ya sa ’yan siyasar ta suke yunkurin dakile hada-hadar Sin mai fifiko bisa manufar kariyar cinikayya.

A wani bangare na daban kuwa, matakin ya kasance wani wasan kwaikwayo na siyasa, duba da cewa, za a gudanar da babban zaben Amurka a bana. Amma, a halin yanzu ana fuskantar hauhawar farashi, da gibin kasafin kudi mai tsanani da dai sauran kalubaloli, don haka dora laifi kan wasu, mataki ne da ’yan siyasar kasar Amurka suka dade suna aiwatarwa.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sana’ar samar da hajoji masu aiki da makamashi mai tsabta ta kasar Sin, ba ma kawai ta samarwa duniya isassun hajoji ba ne, har ma ta sassauta hauhawar farashinsu a duniya, kuma ta taka rawar gani wajen tinkarar sauyin yanayi, da karkata zuwa hanyar samun bunkasuwa ba tare da bata muhalli ba. Don haka dai yunkurin Amurka na dakile kasar Sin ba zai hana ci gabanta ba, sai dai kawai ya fayyace rashin hangen nesa, da kasancewa mai keta ka’idar duniya. (Amina Xu)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IranRashaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3, Sun Sace 130 A Zamfara

Next Post

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Kaddamar Da Taron Koli Na LAS Karo Na 33

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

2 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

3 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

4 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

5 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

7 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Kaddamar Da Taron Koli Na LAS Karo Na 33

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Kaddamar Da Taron Koli Na LAS Karo Na 33

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.