• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotu a birnin Maradi da ke Jamhuriyar Nijar ta yanke wa wasu matasa hukuncin ɗaurin shekara uku-uku a gidan yari, bayan samunsu da laifin naɗa da kuma yaɗa wani bidiyo da ke nuna wasu mata biyu suna madigo.

BBC ta rawaito cewa, wadanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da mata 13 da namiji ɗaya.

  • ‘Ƴar Majalisa Na Burin A Samar Da Tsauraran Dokoki Kan ‘Yan Luwadi Da Madigo A Nijar
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane Fiye Da 130 Cikin Wata Biyu A Nijar

Baya ga hukuncin ɗaurin, kotun ta ci tarar matan su 13 Sefa miliyan ɗaya kowace yayin da aka ci namijin tarar sefa miliyan uku kasancewarsa wanda ke da dandalin manhajar Whatsapp din da aka yadda wannan bidiyon.

Makonni biyu da suka wuce ne dai aka fara gurfanar da mutanen 14 gaban kotun bisa zarginsu da aikata laifin yaɗa abu ta shafukan intanet da ka iya tayar da hankalin jama’a.

Laifin, a cewar lauya mai shigar da ƙara ya saɓawa dokar haramta aikata laifuka ta shafukan intanet.

Labarai Masu Nasaba

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Ya kuma nemi a yi mu su hukunci mafi tsanani na ɗaurin shekaru uku; wanda kuma shi ne kotun ta sanar a ranar Alhamis.

Jami’an tsaro na jandarma ne suka kakkama matasa bayan wani koke da wasu mutane suka yi kan yaɗa bidiyon na batsa.

Dukansu dai an same su da laifin yaɗa abubuwan batsa da nuna tsiraicin ɗan adama da kuma tayar wa jama’a hankali.

Sai dai kotun ta ba su damar ɗaukaka ƙara a cikin kwana 10, kamar yadda dokokin ƙasar suka tanada.

Wannan shari’ar dai ta ja hankalin mutane a ciki da wajen ƙasar ta Nijar saboda yadda aka ce a farkon shari’ar aka yi ta muhawara kan wace doka za a yi amfani da ita wajen yi musu shari’a.

Hakan ya faru ne kasancewar dokokin ba su tanadi hukunci ƙarara da za a iya yankewa wadanda aka samu da aikata laifin luwaɗi ko maɗigo ba.

Ba mamaki wannan ne ya sa aka yi amfani da dokar haramta yaɗa abubuwa masu tayar da hankali a shafukan inta wajen yi musu shari’a.

Sakamakon haka dai yanzu haka wata ƴar majalisar dokokin ƙasar ta gabatar da ƙuduri gaban majalisar da ke neman yin dokar haramta luwadi da maɗigo a ƙasar mai rinjayen Musulmi da ke yammacin Afrika.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuMadigoNijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

A Real Madrid Zan Yi Ritaya Daga Buga Kwallo, Cewar Benzema

Next Post

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Related

Labarai

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

47 minutes ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

2 hours ago
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi
Manyan Labarai

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

3 hours ago
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

13 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

15 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

17 hours ago
Next Post
Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa - Sarkin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.