• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Ɗaure Mutum 14 Kan Yaɗa Bidiyon Maɗigo A Jamhuriyar Nijar

by Muhammad
3 years ago

Kotu a birnin Maradi da ke Jamhuriyar Nijar ta yanke wa wasu matasa hukuncin ɗaurin shekara uku-uku a gidan yari, bayan samunsu da laifin naɗa da kuma yaɗa wani bidiyo da ke nuna wasu mata biyu suna madigo.

BBC ta rawaito cewa, wadanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da mata 13 da namiji ɗaya.

  • ‘Ƴar Majalisa Na Burin A Samar Da Tsauraran Dokoki Kan ‘Yan Luwadi Da Madigo A Nijar
  • Ambaliyar Ruwa Ta Kashe Mutane Fiye Da 130 Cikin Wata Biyu A Nijar

Baya ga hukuncin ɗaurin, kotun ta ci tarar matan su 13 Sefa miliyan ɗaya kowace yayin da aka ci namijin tarar sefa miliyan uku kasancewarsa wanda ke da dandalin manhajar Whatsapp din da aka yadda wannan bidiyon.

Makonni biyu da suka wuce ne dai aka fara gurfanar da mutanen 14 gaban kotun bisa zarginsu da aikata laifin yaɗa abu ta shafukan intanet da ka iya tayar da hankalin jama’a.

Laifin, a cewar lauya mai shigar da ƙara ya saɓawa dokar haramta aikata laifuka ta shafukan intanet.

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

Ya kuma nemi a yi mu su hukunci mafi tsanani na ɗaurin shekaru uku; wanda kuma shi ne kotun ta sanar a ranar Alhamis.

Jami’an tsaro na jandarma ne suka kakkama matasa bayan wani koke da wasu mutane suka yi kan yaɗa bidiyon na batsa.

Dukansu dai an same su da laifin yaɗa abubuwan batsa da nuna tsiraicin ɗan adama da kuma tayar wa jama’a hankali.

Sai dai kotun ta ba su damar ɗaukaka ƙara a cikin kwana 10, kamar yadda dokokin ƙasar suka tanada.

Wannan shari’ar dai ta ja hankalin mutane a ciki da wajen ƙasar ta Nijar saboda yadda aka ce a farkon shari’ar aka yi ta muhawara kan wace doka za a yi amfani da ita wajen yi musu shari’a.

Hakan ya faru ne kasancewar dokokin ba su tanadi hukunci ƙarara da za a iya yankewa wadanda aka samu da aikata laifin luwaɗi ko maɗigo ba.

Ba mamaki wannan ne ya sa aka yi amfani da dokar haramta yaɗa abubuwa masu tayar da hankali a shafukan inta wajen yi musu shari’a.

Sakamakon haka dai yanzu haka wata ƴar majalisar dokokin ƙasar ta gabatar da ƙuduri gaban majalisar da ke neman yin dokar haramta luwadi da maɗigo a ƙasar mai rinjayen Musulmi da ke yammacin Afrika.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi
Labarai

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Next Post
Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa - Sarkin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.