• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Bude Bikin Baje Kolin Fina-Finan Asiya Karo Na 4 A Najeriya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Bude Bikin Baje Kolin Fina-Finan Asiya Karo Na 4 A Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Litinin 21 ga watan Nuwambar nan ne aka kaddamar da baje kolin fina-finan Asiya karo na 4 a Najeriya. Bikin wanda ofisoshin jakadancin kasashen Asiya 9 da suka hada da Sin, da Iran da Koriya ta kudu, da kuma Najeriya suka yi hadin gwiwar shiryawa, ya gudana ne a cibiyar nune-nunen al’adun kasar Sin dake birnin Abuja, fadar mulkin Najeriya.

Cikin jawabinsa yayin bude bikin, jakadan Sin a Najeriya Cui Jianchun, ya ce al’adu su ne ruhin kowace kasa, kuma musayar al’adu tamkar musayar zuciyoyi da rayukan al’ummun kasashen duniya ne. Kaza lika fina-finai na nuna yanayi na sassan al’adun al’ummu daban daban.

  • A Dauki Hakikakin Matakai Domin Kyautata Hulda A Tsakanin Sin Da Amurka

Jakada Cui ya ce dandalin baje kolin fina-finai na hadin gwiwar kasashe daban daban, muhimmiyar hanya ce ta gina dandalin fahimtar al’adun juna, da ma yanayin rayuwar al’ummu, kuma hakan zai ci gaba da ba da gudummawa wajen zurfafa fahimtar juna tsakanin al’ummu, da inganta kawancen kasashe.

Ya ce karkashin hakan, za a iya kyautata fahimtar juna, da inganta kawance dake maye gurbin kyamar juna, kana mutane za su kara rayuwa cikin lumana, kuma duniya za ta samu ci gaba cikin yanayin zaman lafiya. Har ila yau, musayar al’adu kyakkyawar manufa ce da duniya ke son cimmawa, kuma hakan shi ne ainihin dalilin shirya bikin na wannan karo.

Daga nan sai jakada Cui ya shawarci mahukuntan Najeriya da su shirya makamancin wannan biki a Sin, domin baiwa Sinawa damar kallon fina finan Najeriya, tare da kara fahimtar kasar, a matsayinta na babbar kasa a nahiyar Afirka. (Mai Fassarawa: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotun Daukaka Kara Ta Haramtawa Aleiro Da Abdullahi Takarar Sanata A Kebbi

Next Post

Yadda ISWAP Ta Kai Hari Sansanin Sojoji, Mutane Da Dama Sun Mutu A Jihar Borno

Related

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

9 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

14 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

15 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

16 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

17 hours ago
Next Post
Yadda ISWAP Ta Kai Hari Sansanin Sojoji, Mutane Da Dama Sun Mutu A Jihar Borno

Yadda ISWAP Ta Kai Hari Sansanin Sojoji, Mutane Da Dama Sun Mutu A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

June 6, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

June 6, 2025
Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

Ambaliyar Ruwa A Mokwa: Kauyuka 1,249 A Jihohi 30 Na Cikin Hadari — Gwamnatin Tarayya

June 6, 2025
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

June 6, 2025
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 6, 2025
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.