ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
Barau

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (CFR), ya bayyana shirinsa na kai ƙarar kwamitin yaƙin neman zaɓen Gawuna-Garo bisa zargin cewa shi da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, sun karɓi cin hancin dala miliyan 10 domin hana tabbatar da naɗin Abdullahi Garba Ramat a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC).

Wannan bayani ya fito ne daga Comrade Hafizu Sani Liman, jagoran ƙungiyar All Tinubu/Barau Support Groups, yayin taron manema labarai a Kano ranar Juma’a. Liman ya ce zargin “ƙarya ne, kazafi ne kuma ai yi shi ne da nufin ɓata suna,” tare da ƙara wa da cewa “an ƙirƙire shi ne domin rage darajar Sanata Barau a idon jama’a.”

  • Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito cewa, Liman ya bayyana cewa waɗanda ke da hannu a yaɗa wannan zargi — ciki har da Hon. Muhammadu Badaru Umar da Alwan Hassan — duka ƴan jam’iyyar APC ne, amma sun rungumi siyasar ɓata suna maimakon haɗin kai don cigaban jam’iyyar a Kano. Ya kuma jaddada cewa naɗa shugaban NERC na cikin ikon shugaban ƙasa, ba na Majalisar Dattawa ba.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa Sanata Barau ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin an tantance Engineer Ramat yadda ya kamata, inda ya bayyana cewa Kwamitin Wutar Lantarki na Majalisa ƙarƙashin Sanata Enyinnaya Abaribe ya kammala tantancewar kuma zai mika rahoto nan ba da jimawa ba.

Liman ya ce lauyoyin Sanata Barau sun samu umarni da su fara  shirin kai ƙarar kotu kan masu yaɗa wannan “ƙarya mai hatsari,” yana mai kira ga jama’ar Kano da su yi watsi da zargin. Ya ƙare da cewa Barau “na ci gaba da zama abin koyi ta fuskar gaskiya da aiki tukuru,” tare da nuna cewa “duk wani kazafi ba zai hana shi hidima ga al’ummar Kano da Nijeriya ba.”

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Barau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu - Gwamna Lawal

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.