ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barau Zai Yi Ƙarar Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Gawuna/Garo Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Dala Miliyan 10

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Barau

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin (CFR), ya bayyana shirinsa na kai ƙarar kwamitin yaƙin neman zaɓen Gawuna-Garo bisa zargin cewa shi da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, sun karɓi cin hancin dala miliyan 10 domin hana tabbatar da naɗin Abdullahi Garba Ramat a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC).

Wannan bayani ya fito ne daga Comrade Hafizu Sani Liman, jagoran ƙungiyar All Tinubu/Barau Support Groups, yayin taron manema labarai a Kano ranar Juma’a. Liman ya ce zargin “ƙarya ne, kazafi ne kuma ai yi shi ne da nufin ɓata suna,” tare da ƙara wa da cewa “an ƙirƙire shi ne domin rage darajar Sanata Barau a idon jama’a.”

  • Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito cewa, Liman ya bayyana cewa waɗanda ke da hannu a yaɗa wannan zargi — ciki har da Hon. Muhammadu Badaru Umar da Alwan Hassan — duka ƴan jam’iyyar APC ne, amma sun rungumi siyasar ɓata suna maimakon haɗin kai don cigaban jam’iyyar a Kano. Ya kuma jaddada cewa naɗa shugaban NERC na cikin ikon shugaban ƙasa, ba na Majalisar Dattawa ba.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa Sanata Barau ya taka muhimmiyar rawa wajen ganin an tantance Engineer Ramat yadda ya kamata, inda ya bayyana cewa Kwamitin Wutar Lantarki na Majalisa ƙarƙashin Sanata Enyinnaya Abaribe ya kammala tantancewar kuma zai mika rahoto nan ba da jimawa ba.

Liman ya ce lauyoyin Sanata Barau sun samu umarni da su fara  shirin kai ƙarar kotu kan masu yaɗa wannan “ƙarya mai hatsari,” yana mai kira ga jama’ar Kano da su yi watsi da zargin. Ya ƙare da cewa Barau “na ci gaba da zama abin koyi ta fuskar gaskiya da aiki tukuru,” tare da nuna cewa “duk wani kazafi ba zai hana shi hidima ga al’ummar Kano da Nijeriya ba.”

LABARAI MASU NASABA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Barau
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
  • Abubakar Sulaiman
    Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

MASU ALAKA

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
Manyan Labarai

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal

Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu - Gwamna Lawal

LABARAI MASU NASABA

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026
Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

Tsarin Kirkire-Kirkire Na Sin Na Kara Kuzari Ga Makomar Masana’antun Duniya

June 27, 2026
Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.