• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Ma’aikatan NIMC Na Bogi Da Ke Yi Wa Wadanda Ba ‘Yan Nijeriya Katin Dan Kasa

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
An Cafke Ma’aikatan NIMC Na Bogi Da Ke Yi Wa Wadanda Ba ‘Yan Nijeriya Katin Dan Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar tsaro ta bayyana cewa dakarunta tare da hadin gwiwar hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya NIS da rundunar ‘yansandan Nijeriya sun cafke wasu jami’an bogi biyu na hukumar ba da shaida katin dan kasa a Jamhuriyar Nijar. 

Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaro, Manjo-Janar Musa Danmadami, ya bayyana hakan ne ga manema labarai a taron mako biyu kan ayyukan sojojin Nijeriya tsakanin 6 zuwa 20 ga Oktoba, 2022 a hedikwatar tsaro da ke Abuja ranar Alhamis.

  • Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 
  • Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Gagamari a Jamhuriyar Nijar a lokacin da suke yi wa wadanda ba ‘yan Nijeriya rijista ba tare da sanya su cikin ma’adanar bayanai ta Nijeriya ba.

Danmadami ya zayyana kayayyakin da jami’an tsaro suka kwato daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da: Na’urar rajista ta kasa (NIN), na’urar buga kati, na’urar bin diddigin kwamfuta da injin janareta da dai sauransu.

“A ranar 13 ga Oktoba, 2022, sojoji tare da rundunar ‘yansandan Nijeriya da jami’an NIS sun kama wasu jami’an hukumar kula da bayanan sirri na kasa (NIMC) guda 2 da ake zargin na bogi ne.

Labarai Masu Nasaba

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

“An bayyana cewa wadanda ake zargin sun ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Gagamari da ke Jamhuriyar Nijar ne domin yin rijistar wadanda ba ‘yan Nijeriya ba a sansanin ‘yan gudun hijirar.

“Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da na’urar rijista ta kasa (NIN), na’urar buga kati, na’urar bin diddigin kwamfuta da injin janareta da dai sauransu.”

Da yake tsokaci game da ci gaban yayin gabatar da tambayoyi daga ‘yan jarida, tsohon Daraktan DMO, Manjo-Janar Benard Onyeuko, ya ce za a bankado aniyar jami’an bogi idan an kammala bincike.

Ya ce wannan wani sabon abu ne da sojoji suka samu don haka ya kamata a yaba wa rundunar soji.

“Rundunar sojin ta cancanci a yaba mata bisa nasarar da ta samu wajen kame wadannan masu laifi a kasar waje.”

Onyeuko, wanda yanzu shi ne Daraktan sayan kayayyaki a hedikwatar tsaro ya kara da cewa, “A cikin wannan yanayi, yanzu an kama su, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike, wanda ya hada da duk wanda ke da alaka da wannan badakala.

Ya kara da cewa, “Za a bayyana sakamako idan aka kammala bincike, amma a lura cewa wannan wani sabon abu ne, kuma ina ganin ya kamata a yabawa sojojin kasar kan hakan.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DakaruJamhuriyar NijarMa'aikatan BogiNIMCNINSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Next Post

Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

Related

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

16 minutes ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

46 minutes ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

6 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

17 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

19 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

24 hours ago
Next Post
Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

LABARAI MASU NASABA

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.