• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

An Cafke Ma’aikatan NIMC Na Bogi Da Ke Yi Wa Wadanda Ba ‘Yan Nijeriya Katin Dan Kasa

by Sadiq
4 months ago
in Manyan Labarai
0
An Cafke Ma’aikatan NIMC Na Bogi Da Ke Yi Wa Wadanda Ba ‘Yan Nijeriya Katin Dan Kasa

Hedikwatar tsaro ta bayyana cewa dakarunta tare da hadin gwiwar hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya NIS da rundunar ‘yansandan Nijeriya sun cafke wasu jami’an bogi biyu na hukumar ba da shaida katin dan kasa a Jamhuriyar Nijar. 

Darakta mai kula da ayyukan yada labarai na tsaro, Manjo-Janar Musa Danmadami, ya bayyana hakan ne ga manema labarai a taron mako biyu kan ayyukan sojojin Nijeriya tsakanin 6 zuwa 20 ga Oktoba, 2022 a hedikwatar tsaro da ke Abuja ranar Alhamis.

  • Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 
  • Wata Kungiya Ta Yi Barazanar Maka Kungiyar Kwadago A Kotu A Jihar Kebbi

Ya ce an kama wadanda ake zargin ne a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Gagamari a Jamhuriyar Nijar a lokacin da suke yi wa wadanda ba ‘yan Nijeriya rijista ba tare da sanya su cikin ma’adanar bayanai ta Nijeriya ba.

Danmadami ya zayyana kayayyakin da jami’an tsaro suka kwato daga hannun wadanda ake zargin da suka hada da: Na’urar rajista ta kasa (NIN), na’urar buga kati, na’urar bin diddigin kwamfuta da injin janareta da dai sauransu.

“A ranar 13 ga Oktoba, 2022, sojoji tare da rundunar ‘yansandan Nijeriya da jami’an NIS sun kama wasu jami’an hukumar kula da bayanan sirri na kasa (NIMC) guda 2 da ake zargin na bogi ne.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

“An bayyana cewa wadanda ake zargin sun ziyarci sansanin ‘yan gudun hijira na Gagamari da ke Jamhuriyar Nijar ne domin yin rijistar wadanda ba ‘yan Nijeriya ba a sansanin ‘yan gudun hijirar.

“Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da na’urar rijista ta kasa (NIN), na’urar buga kati, na’urar bin diddigin kwamfuta da injin janareta da dai sauransu.”

Da yake tsokaci game da ci gaban yayin gabatar da tambayoyi daga ‘yan jarida, tsohon Daraktan DMO, Manjo-Janar Benard Onyeuko, ya ce za a bankado aniyar jami’an bogi idan an kammala bincike.

Ya ce wannan wani sabon abu ne da sojoji suka samu don haka ya kamata a yaba wa rundunar soji.

“Rundunar sojin ta cancanci a yaba mata bisa nasarar da ta samu wajen kame wadannan masu laifi a kasar waje.”

Onyeuko, wanda yanzu shi ne Daraktan sayan kayayyaki a hedikwatar tsaro ya kara da cewa, “A cikin wannan yanayi, yanzu an kama su, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike, wanda ya hada da duk wanda ke da alaka da wannan badakala.

Ya kara da cewa, “Za a bayyana sakamako idan aka kammala bincike, amma a lura cewa wannan wani sabon abu ne, kuma ina ganin ya kamata a yabawa sojojin kasar kan hakan.”

Tags: DakaruJamhuriyar NijarMa'aikatan BogiNIMCNINSojoji
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Firaministan Birtaniya, Liz Truss Ta Yi Murabus 

Next Post

Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

Related

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

1 day ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

1 day ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

1 day ago
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike
Manyan Labarai

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

2 days ago
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari
Manyan Labarai

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

2 days ago
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

2 days ago
Next Post
Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

Tsarin Zamanintar Da Aikin Noma Na Sin Ya Gaggauta Bunkasuwarta Da Ma Duniya Baiki Daya

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.