• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Matashin Da Ya Yi Lalata ‘Yar Makocinsa Mai Shekara Takwas

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Cafke

Rundunar ‘yansandan a Jihar Ogun ta kama wani yaro dan shekara 17 mai suna Jamiu Adebayo da laifin lalata da ‘yar makocinsa ‘yar shekara takwas a unguwar Aregbe dake Abeokuta, babban birnin jihar.

Jaridar PUNCH Metro ta gano cewa wanda ake zargin ya yaudari yarinyar zuwa dakin iyayensa, inda ya umarce ta da ta cire mata rigarta, sannan ya yi lalata da ita.

  • Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje
  • Jarumin Bollywood Saif Ali Khan Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Rundunar ‘yansandan ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an kama wanda ake zargin, kuma ana ci gaba da gudanar da kwakkwaran bincike don gano musabbabin aikata laifin.

PUNCH Metro ta samu labari daga mai magana da yawun ‘yansandan, Omolola Odutola, cewa mahaifiyar wacce aka lalata, mai suna Olabode, ba ta nan a lokacin da makota suka kira ta domin sanar da ita cewa jini na fita daga al’aurar ‘yarta.

Rundunar ‘yansandan ta ce Olabode ta shaida wa ‘yansanda cewa ta yi matukar kaduwa da fargaba a lokacin da ta gano jini na fita daga al’aurar ‘yarta a lokacin da ta isa wurin.

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

A kokarin da wakilinmu ya yi na gano musabbabin zubar jinin, ya gano cewa, duk kokarin da aka yi na shawo kan yarinyar ta bayyana abin da ya faru ya ci tura, domin ta sha nanata irin wannan bayanin da ta yi wa makotanta cewa itace ta raunata al’aurarta. .

Bayan matsin lamba da lallashi, an ruwaito wacce abin ya shafa ta shaida wa mahaifiyarta cewa wani matashi mai suna Adebayo mai shekaru 17 da ke zaune a ginin makota ne ya yi mata fyade.

Rundunar ta bayyana cewa wanda ake zargin ya amsa laifin da ake zarginsa da shi inda ya shigar da ita cikin dakinsu, inda ake zargin ya hau kanta ya yi lalata da ita.

Odutola ya ce, “Wadanda ake zargin ya dauke ta zuwa bandakinsu domin ta wanke jinin, sannan ya umarce ta da ta sauya rigarta. Ya kuma lallashe ta kan ta yi karya wai sanda ce ta yi mata rauni a al’aurarta.

“Jami’an tsaro sun yi gaggawar kama wanda ake zargin. An bayar da fom na likita ga wacce abin ya shafa da mahaifiyarta don a duba su kuma su ba da rahoto. A halin yanzu ana gudanar da bincike na farko.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
Manoma A Jihar Benuwe Sun Koka Kan Jinkirin  Saukar Ruwan Sama

An Kashe Manomi A Binuwai Bayan An Karbi Kudin Fansa Naira Miliyan 5.5

LABARAI MASU NASABA

TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.