• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Labarai
0
Yadda Kuncin Rayuwa Da Matsalar Tattalin Arziki Ke Kara Haifar Da Rikice-rikice Tsakanin ‘Yan Haya Da Masu Gidaje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tabarbarewar tattalin arziki a Nijeriya ya haifar da karin karancin biyan kudin haya yayin da masu hayar ke ci gaba da biyan kudin haya a duk shekara.

Yayin da hauhawar farashin kayayyaki ya kai kashi 34.6 cikin 100 da kuma yawan rashin aikin yi, da yawa daga cikin masu haya suna kokawa don biyan bukatunsu, lamarin da ya tilasta wa masu gidaje fuskantar karuwar basussuka.

  • Kotu Ta Ɗaure Wasu Mutane 4 Da Ake Zargi Da Satar Birkin Jirgin Sama Guda 80 A Kano
  • Bajintar Aiki: Majalisar Dattawa Ta Jinjina Wa Ministan Yaɗa Labarai

Masu haya a Nijeriya na kara kokawa kan yadda farashin hayan ya tashi a yayin da ake fama da matsalar tsadar rayuwa.

Yayin da hauhawar farashin kaya ya kai kashi 34.6 cikin 100 a watan Nuwambar 2024, masu gidaje sun kara kudin hayar gida da kashi 100 bisa 100 a manyan garuruwa kamar Legas, lamarin da ya kara ta’azzara matsalar kudi ga masu haya da da kuma raguwar kudaden shiga.

Rahotanni sun nuna cewa kusan kashi 80 cikin 100 na kadarorin da wasu masu gidajen ke kula da su ne ke da karancin masu haya, wanda hakan ya haifar da takaici da kuma tunani sayar da su.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Duk da kokarin da gwamnati ke yi na habaka biyan kudi na wata-wata, kudaden na haya na shekara-shekara karuwar kudaden haya na kara dagula lamarin.

Masu gidajen na kara bayyana takaicin rashin biyan kudin haya, wanda hakan ya sa wasu ke tunanin sayar da kadarorinsu. Mutane da yawa suna ba da rahoton matsaloli wajen karbar kudin hayar, musamman daga masu biyan kudin haya na dogon lokaci wadanda suka ambata a baya kan biyan kudi.

An dai bayyana dokar ba da hayar gidaje a Jihar Legas a matsayin wani shamaki wanda ke zama kalubale ga masu gidaje na su kwato kadarorinsu daga hannun wadanda suka gaza biyan kudin haya.

Sakamakon haka, masu zuba jari suna barin kasuwar saye-sayarwa, domin fargabar dawowar dogon lokaci a kan zuba jari saboda tabarbarewar tattalin arziki da tsadar rayuwa. Wasu masu gidaje suna tunanin kara kudin hayar don rage asara.

Masana dai na nuni da cewa lamarin zai kara tabarbare ne in ba tare da sa hannun gwamnati ba, kamar yadda ake sarrafa haya, da barin masu gidajen haya a cikin wani yanayi na tsadar kayayyaki da kuma rage karfin saye da sayarwa.

Duk da wadannan kalubale, masu haya a jihar Legas sun nuna sha’awar biyan hayar shekara-shekara fiye da biyan hayar wata-wata kamar yadda binciken kasuwar gidaje na BuyLetLibe 2024 ya yi kiyasi.

Hakan dai na faruwa ne duk da hayar da ake yi ba bisa ka’ida ba da ke kawo cikas ga zuba hannun jari na cikin gida da na waje a fannin kadarori na kasar.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, tabarbarewar tattalin arziki a kasar, kamar hauhawar farashin kayayyaki, na kawo cikas ga harkokin zuba jari na cikin gida da na waje a fannin.

Wannan ma kamar yadda rahoton ya yi hasashen cewa irin wannan dabarar za ta haifar da gasa ga rukunin gidaje da ake da su a wuraren da ake bukata. Rahoton na BuyLetLibe mai taken ‘Rahoton Mazauna Gidaje’ ya bayyana cewa kashi 63 cikin 100 na masu karba sun fi son biyan haya na shekara-shekara akan kudin wata.

Bayanan binciken ya ci karo da ra’ayoyin jama’a da kuma shirye-shiryen gwamnatin Jihar Legas na bullo da biyan kudin haya ta intanet a duk wata a bangaren gidaje na jihar.

A cewar rahoton, kusan kashi 62.6 cikin 100 na masu amsa tambayoyinmu na Legas har yanzu sun fi son biyan hayar shekara fiye da sauran hanyoyin biyan kudi.

Gwamnatin jihar ta bayyana hakan ne a cikin wata takarda mai suna “EKO Rebenue Plus Summit,” mai taken “Bude Sabbin hanyoyin Haraji Ga Jihar Legas.” Shirin ya zayyana samar da Naira biliyan 2.5 a duk shekara daga masu biyan kusan 100,000 duk shekara.

Rahoton ya nuna cewa gwamnatin Jihar Legas za ta mallaki wannan tsarin na zamani, tare da hukumomi kamar ma’aikatar gidaje ta Jihar Legas da sauran MDAs a matsayin abokan aikin fasaha.

Wani kashi 36.4 kuma ya nuna sha’awar motsawa cikin watanni shida zuwa 12 masu zuwa. Rahoton ya yi nuni da cewa, fifikon hayar ‘yan Legas na nuna tsananin bukatar gidaje masu araha a jihar.

Bugu da kari, binciken ya nuna cewa mafi yawan ‘yan Legas sun gwammace su biya tsakanin Naira miliyan 1 da miliyan 3 a matsayin biyan kudin hayar shekara-shekara, kamar yadda kashi 34.5 na wadanda suka amsa suka bayyana.

Haka kuma, kashi 11.8 bisa 100 na masu karba sun fi son farashin haya tsakanin Naira 100,000 zuwa Naira 500,000, yayin da kashi 26.4 bisa 100 sun fi son biyan kudin haya a duk shekara tsakanin Naira 500,000 zuwa Naira miliyan daya.

A daya bangaren kuma, kashi 7.3 cikin 100 na wadanda aka bayyana za su iya biyan kudin hayar Naira miliyan 5 zuwa miliyan 10 domin kashi 20 cikin 100 za su zabi biyan kudin hayar tsakanin Naira miliyan uku zuwa miliyan biyar.

Dangane da girman gidaje, yawancin ’yan Legas da aka ruwaito a cikin binciken sun nuna fifikon daki mai gadaje 2 ad daki mai gadaje 3 da kashi 38.2 cikin dari da kashi 35.5 bisa dari bi da bi.

Hakanan, kashi 16.4 cikin dari da kashi 9.2 cikin dari na masu amsawa sun zabi dakuna 4 da dakuna 1 bi da bi a matsayin nau’in gidan da suka fi so. Dangane da yanayin da ake ciki a fannin kadarori na Legas, rahoton ya yi hasashen cewa kasuwar gidaje a Legas za ta ci gaba da baje kolin gidajen zama duk da matsalar tabarbarewar tattalin arziki da aka samu a shekarar da ta gabata.

An yi nuni da cewa, saurin karuwar farashin zai ragu a rabin na biyu na shekara idan aka kwatanta da yadda aka samu karuwa a cikin shekara daya da ta gabata.

Rahoton ya kuma bayyana cewa, tabarbarewar tattalin arziki a kasar nan (habakar hauhawar farashin kayayyaki) na kawo cikas ga zuba jari na cikin gida da na waje a fannin, inda masu zuba jari ke daukar hanyar “jira ku gani”.

Irin wannan dabarun ana hasashen za su haifar da gasa ga rukunin gidaje da ake da su a wuraren da ake bukata.

Ta kuma jaddada cewa, duk da matsalolin tattalin arziki, harkar gidaje za ta bunkasa nan da shekaru masu zuwa saboda karuwar yawan jama’a da kuma saurin karuwar birane.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HayaMasu Gida
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Masarautar Kano Ya Sake Daukar Sabon Salo

Next Post

Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

4 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

6 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

7 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

10 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

13 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

14 hours ago
Next Post
Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin

Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.